• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Cibiyar Raya Noma Da Sin Ta Gina A Najeriya

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tasirin Cibiyar Raya Noma Da Sin Ta Gina A Najeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon makon nan ne gwamnatin Sin ta mikawa gwamnatin Najeriya sabuwar cibiyar binciken harkokin noma, wadda aka kammala ginin ta a garin Bwari dake kusa da birnin Abuja fadar mulkin kasar. Cibiyar dai daya ce daga ayyuka daban daban da kasar Sin ke tallafawa gudanarwa a Najeriya, a wani bangare na cika alkawarun da Sin din ta jima tana dauka, na agazawa abokan tafiyar ta wato kasashe masu tasowa.

Masana sun tabbatar da cewa, wannan cibiya ta bincike, za ta taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa, da fadada ci gaban ayyukan noma a kasar mafi yawan jamaa a Afirka. Ko shakka babu, wannan cibiya za ta yi babban tasiri ga alummar Najeriya, musamman manoma, da hukumomin kasar masu nasaba da harkokin noma, da ma matasa wadanda a nan gaba za su samu zarafin shiga sanaar noma gadan gadan.

  • Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Karu Da 8.6% Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamba

Mafiya yawa daga mazauna birane musamman matasa dake son fara sanaoi a Najeriya, ba su cika rungumar sanaar noma ba, duba da wahalhalun dake tattare da sanaar, ga kuma karancin dabarun zamani na gudanar da sanaar wanda kan haifar da karancin ribi, ko fuskantar asara yayin da ake gudanar da ita bisa salon gargajiya.

Sabuwar cibiyar dai na kunshe da abubuwa na binciken fasahohin zamani da ake amfani da su a harkar noma, da wuraren ba da horo ko samun kwarewar makamar aiki. Kaza lika ta kunshi kayan aiki na nazari domin saukaka noma a zamanance, ta yadda manazarta za su samu damar zakulo dabaru na sauya akalar ayyukan noma daga na gargajiya zuwa na zamani, da fito da dabarun bunkasa yawan hatsi da manoma za su iya nomawa a Najeriya, da ma fadada sassan noma da kiwo daban daban. Har ila yau, akwai dakunan gwaje gwaje, da madatsar ruwa, da cibiyar nune-nunen yadda ake sarrafa amfanin gona, da cibiyar samar da makamashi da sauran su.

Hakika wannan sabuwar cibiya, shaida ce dake nuni ga manyan nasarori da Sin tare da Najeriya suke samu, karkashin dadadden hadin gwiwa, da zumuncin dake tsakanin sassan biyu.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Tabbas, bisa abubuwan da aka tanada a wannan cibiya, yan Najeriya musamman manoma, za su ci babbar gajiya daga fasahohin zamani na bincike da gwaje gwaje, kuma cibiyar za ta ci gaba da zama wata alama, game da kyakkyawar dangantaka dake tsakanin Sin da Najeriya cikin tsawon lokaci. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Shirye Nake Don Yin Muhawara Tun Daga Safe Har Zuwa Dare – Tinubu

Next Post

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

10 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

11 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

13 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

14 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

15 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

16 hours ago
Next Post
Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.