ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Cibiyar Raya Noma Da Sin Ta Gina A Najeriya

by CMG Hausa
4 years ago
Noma

A farkon makon nan ne gwamnatin Sin ta mikawa gwamnatin Najeriya sabuwar cibiyar binciken harkokin noma, wadda aka kammala ginin ta a garin Bwari dake kusa da birnin Abuja fadar mulkin kasar. Cibiyar dai daya ce daga ayyuka daban daban da kasar Sin ke tallafawa gudanarwa a Najeriya, a wani bangare na cika alkawarun da Sin din ta jima tana dauka, na agazawa abokan tafiyar ta wato kasashe masu tasowa.

Masana sun tabbatar da cewa, wannan cibiya ta bincike, za ta taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa, da fadada ci gaban ayyukan noma a kasar mafi yawan jamaa a Afirka. Ko shakka babu, wannan cibiya za ta yi babban tasiri ga alummar Najeriya, musamman manoma, da hukumomin kasar masu nasaba da harkokin noma, da ma matasa wadanda a nan gaba za su samu zarafin shiga sanaar noma gadan gadan.

  • Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Karu Da 8.6% Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamba

Mafiya yawa daga mazauna birane musamman matasa dake son fara sanaoi a Najeriya, ba su cika rungumar sanaar noma ba, duba da wahalhalun dake tattare da sanaar, ga kuma karancin dabarun zamani na gudanar da sanaar wanda kan haifar da karancin ribi, ko fuskantar asara yayin da ake gudanar da ita bisa salon gargajiya.

ADVERTISEMENT

Sabuwar cibiyar dai na kunshe da abubuwa na binciken fasahohin zamani da ake amfani da su a harkar noma, da wuraren ba da horo ko samun kwarewar makamar aiki. Kaza lika ta kunshi kayan aiki na nazari domin saukaka noma a zamanance, ta yadda manazarta za su samu damar zakulo dabaru na sauya akalar ayyukan noma daga na gargajiya zuwa na zamani, da fito da dabarun bunkasa yawan hatsi da manoma za su iya nomawa a Najeriya, da ma fadada sassan noma da kiwo daban daban. Har ila yau, akwai dakunan gwaje gwaje, da madatsar ruwa, da cibiyar nune-nunen yadda ake sarrafa amfanin gona, da cibiyar samar da makamashi da sauran su.

Hakika wannan sabuwar cibiya, shaida ce dake nuni ga manyan nasarori da Sin tare da Najeriya suke samu, karkashin dadadden hadin gwiwa, da zumuncin dake tsakanin sassan biyu.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Tabbas, bisa abubuwan da aka tanada a wannan cibiya, yan Najeriya musamman manoma, za su ci babbar gajiya daga fasahohin zamani na bincike da gwaje gwaje, kuma cibiyar za ta ci gaba da zama wata alama, game da kyakkyawar dangantaka dake tsakanin Sin da Najeriya cikin tsawon lokaci. (Saminu Alhassan)

Noma
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.