• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tausayin Annabi Muhammadu (SAW) Ga Al’ummarsa

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
in Dausayin Musulunci
0
Manzon Allah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An ruwaito cewa, wani Balaraben kauye ya zo wurin Annabi ((SAW)) yana neman wani abu, sai Annabi ((SAW)) ya ba shi abin da ya samu a wannan lokaci, sannan Annabi ((SAW)) ya yi masa wasan kakaci da cewa “Na Kyautata maka ya kai Balaraben kauye?”, sai ya ce, “Ina sam baka kyautata min”, sai Sahabbai ransu ya baci suka yi fushi, suka tashi suna nufin farmasa, sai Annabi ((SAW)) ya yi ishara gare su, su kyale shi, sai Annabi ((SAW)) ya tashi ya shiga cikin gida ya kara nemo wani abu ya ba shi sannan ya sake tambayarshi “Na Kyautata maka ya kai Balaraben kauye?”, sai ya ce “Na’am lallai ka kyautata min yanzun, Allah ya saka maka ya dan’uwana da alkhairi”. Sai Annabi ((SAW)) ya ce masa, “ka fada wani abu wanda ya bata wa Sahabbaina rai, ina so ka sake fadar addu’ar da ka yi min a gabansu, sabida abinda ke cikin zuciyoyinsu a gare ka ya fita”. Sai ya ce, zan fada musu.

Wata rana, da Balaraben ya dawo wurin Annabi (SAW) yayin da yake zaune cikin sahabbansa, sai Annabi (SAW) ya ce, wannan Balaraben nan ya zo, mun bashi kyauta sai ya nemi a kara masa, bayan mun kara masa sai ya raya a zuciyarsa cewa, abin da aka kara masa ya wadatar da shi, Balarabe haka aka yi? Annabi ya tambaye shi, sai ya amsa da cewa, Na’am Ya Rasulallahi haka aka yi, Allah ya saka maka, ka zama dan’uwa. Sai Annabi (SAW) ya ce misalina da wannan Balaraben kamar wani mutum ne da yake da Rakuma ta tsinke ta yi Daji, sai mutane suka bi ta a guje suna son su kamo ta, sai ya zama wannan bin da suke yi mata ba ya kara mata komai sai gudu, da mai rakumin ya ga ya kusa asarar rakumarsa, sai ya kira masu bin ta, ya ce su dawo su kyale ta, na san yadda zan yi in kama rakumata. Sai Mutumin ya shiga gabanta, ya tsugunna kamar ya dibo mata abinci, sai Taguwar ta zo ta tsugunna a gare shi.

  • Daukakar Nasaba Da Girman Garin Annabi Muhammadu (SAW)

Annabi (SAW) ya ce, da na kyale ku lokacin da Balaraben nan ya fada wannan maganar kun far masa kun kashe shi da sai ya shiga wuta, amma yanzun zai mutu da Imani ya shiga Aljannah.

An yi wani Malami mai kudi (Mai Littafin Risala) da shi da wani waliyyi masanin Alkur’ani har yana tasarrufi da Alkur’ani, Zaki ne abin hawanshi, macijiya ce bulalar da yake dukan Zakin da ita, wata rana sai ya ji labarin wannan Malami mai kudi kuma masanin Alkur’ani ne, sai ya kawo masa ziyara don samun Ilimi cikin Alkur’ani. Ya tambaya ina Malam yake, sai aka ce yana gidan Sarki, sai ya ga wata Mace tana shara a Masallaci, ya tambaya wacece wannan, aka ce masa Mahaifiyar Malam ce, sai ya raya a zuciyarsa cewa wannan Malamin dan Duniya ne kawai, yana gidan Sarki kuma Mahaifiyarsa ce ke share masa masallaci, yana jiran Malam, sai ga Malam ya iso a kan doki wani tsoho ya rike masa linzami ya sauka, sai yace wannan tsohon kuma wane ne, sai aka ce masa mahaifin Malam ne, kawai sai ya yi fushi ya juya ya wuce, bayan ya koma wurin zakinsa zai hau, sai Zakin ya bude baki yana nufin far masa, sai ya fahimci cewa, lallai akwai wata Magana, sai ya yi hakuri ya koma har suka hadu da Malam, ya bayyana masa irin abubuwan da suka faru da shi bayan ya yi fushi ya wuce.

Sai Malam ya bayyana masa cewa, yana zuwa fada ne sabida Sarkin Garin ba ya adalci sai in ya gan shi, shi kuma sai ya daura wa kansa kullum sai yaje,” Sarkin ba ya so ya gan ni ni kuma dole sai na je”. Sharar Masallaci kuma, Hadisin Annabi (SAW) ne wanda yake cewa, Duk mai sharar Masallaci, Wuta ba za ta ci wannan jiki ba, ni kuma sai na yi kwadayin Allah ya tseratar da Mahaifiyata zuwa Aljannah. Batun galan-galan na Giya kuma da ake shiga da su gidana, na yi wa’azi jama’a su daina shan giya sun ki, ni kuma ina da kudi, sai na yanke shawarar saye giyar garin baki daya, sai na haka rami a cikin gidana, nake zubarwa.

Labarai Masu Nasaba

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

Batun mahaifina na rike min linzamin doki in zan hau ko kuma in zan sauka, a Hadisin Annabi (SAW), ya ce, duk mai rike wa Malami Linzamin Dabba, wuta ba za ta ci shi ba, ni kuma sai na zabi Mahaifina a kan wannan Daraja.

Sai malamin Alkur’ani ya ce, na Fahimta, Littafin Risala na ji Labari na zo nema, sai ya ce masa, ta fi zan turo maka. A ruwa ya jefa littafin har ya isa garin Malam Mai Alkur’ani.
An ruwaito daga Annabi (SAW) yana cewa “Kar wani daga cikinku ya isar min a kan sahabbaina, kar wani ya zo ya gaya min laifin wani daga cikin sahabbaina, ina so in dinga fitowa zuwa gare ku, babu bacin rai da kowa a cikin kirjina” sai dai abin da zai cuci Jama’a dole a fada.

Yana daga tausayin Annabi (SAW) a kan Al’ummarsa, tausaya da saukakawarsa a gare su. Da yawa ya ki wasu abubuwa tsoron kar a wajabta wa al’ummarsa wannan abin, kamar fadinsa inda yake cewa “Ba don kar in tsananta wa al’ummata ba, da na umarce su da yin Asiwaki (ko makilin) duk yayin Alwala”. Akwai kuma lamarin Sallar dare ta watan Ramadana. Watan Ramadana ya kama, wata rana sai Annabi (SAW) ya shigo masallaci da daddare ya kabbara Sallah, wadanda suke cikin Masallacin, sai suka bi shi Jam’i aka yi Tarawihi, da safe sai suka bawa abokanansu labarin Sallar, da dare ya yi, sai Masallaci ya cika, Annabi (SAW) ya yi Sallar Tarawihi da su, wani daren, Labari ya yadu duk Birni da Kauye, Sahabbai ta ko’ina sun cika Masallaci, sai Annabi (SAW) ya ki fitowa wannan daren, Bayan Safiya ta yi, sai wasu daga cikin sahabbai suka ce, Ya Rasulallahi, jiya Masallaci ya cika sosai muna ta jira ka fito ka yi mana sallah, Annabi (SAW) yace “Da na fito da an wajabta muku wannan Sallar.”
Yana daga cikin tausayawa da saukakawa al’ummarsa, haninsa da jera Azumi biyu a jere ba shan ruwa amma shi yana yin sama da biyu.

Da kinsa ga shiga Ka’aba a aikin hajji, sabida kar kowane Alhaji ya ce dole sai ya shiga Ka’aba in ya je aikin Hajji. A ranar Fat’hu Makkah, bayan ya fito Ka’aba sai aka ga ransa a bace, bayan an tambaye shi me ya sa? Sai ya ce, kar Al’ummata ta raya dole sai ta shiga Ka’aba in ta yi aikin Hajji, wannan Sunnata ce kawai. Sayyada A’isha ta ce masa, Ya Rasulallahi ni ma ina son in shiga Ka’aba, sai yace mata, bari dare ya yi, bayan ya dauko ta a daren, sai ya shigar da ita Hijru Isma’ila ya ce nan ma, a da Ka’aba ne.
Annabi (SAW) ya roka wurin Ubangiji cewa, duk wanda ya bata masa rai har ya yi masa tir, Allah ya maida wannan ya zama shiriyarsa da rahama a gare shi.

Annabi (SAW) ya kasance in yana Sallah ya ji kukan yaro, sai ya yi gaggawa wurin takaita Sallar. Yayin da mutanen Annabi (SAW) suka karyata shi, Mala’ika Jibrilu ya zo masa, ya ce, Ubangijinka ya umarci Mala’ika mai kula da Duwatsu ya yi maka duk abin da ka umurce shi, sannan Mala’ikan ya yi Sallama ga Annabi (SAW) ya ce, ya Annabin Allah ba ni umarnin yadda kake so in hallaka su, sai Annabi (SAW) ya ce masa, ina kwadayi a tsatsonsu a samu wanda zai bi ni da gaskiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kason Farko Na Tallafin Gaggawa Da Sin Ta Aike Ya Isa Türkiyya

Next Post

Babu Zakka A Cikin Dukiyar Haram!

Related

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

7 days ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

2 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

3 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (2): Kyawawan Dabi’u Ke Fayyace Tsoron Allah A Musulunci

4 weeks ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (1)

1 month ago
Yadda Azumi Yake Sa Tsoron Allah
Dausayin Musulunci

Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

2 months ago
Next Post
Mace Za Ta Iya Bai Wa Mijinta Zakkah?

Babu Zakka A Cikin Dukiyar Haram!

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.