ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (3)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
8 months ago
Maulidin

Manzon Allah (SAW) rahama ne ga halitta gaba daya, da mun karanta fatiha kuma sai mu ji tana cewa “godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halitta ” ba wai Ubangijin musulmai su kadai ba. Shi “kitabu” (hukunce hukunce na Shari’a) shiriya ne ga masu tsoron Allah (hudan lil muttakiina), Amma “kur’anu” (ilmi) kuwa shi shiriya ne ga halitta (hudan linnaasi). To mungode Allah yan’uwa, wannan shi ne sakon Annabi Muhammad (SAW), mu rike wadannan abubuwa uku, mu yi ta murna a kansu; na farko, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam shi ne cikamakon ma’aika, na biyu sakonsa (SAW) shine cikamako; don haka dole ya bambanta da saura, sannan na uku Manzon Allah (SAW) rahma ne ga halitta; don haka komai na sa yafi sauki don ya tafi da ‘yan Adam baki daya. To mu rike wannan: idan za mu yi kira, to mu rika yin kira yadda Annabi Muhammad (SAW) yake yi, mu san wannan addini na halitta ne gaba daya ba wai iya mu kadai ba, ba wai iya wata kabila kadai ko wata kasa kadai ba.

Don haka ne Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya kafa wayewa da birnantaka (cibilization and culture). Wannan ne ya sa Makkah ta kasa karbar sakon Manzon Allah (SAW) cikin hanzari ba saboda tsohon gari ne (ma’ana “ummul-kurah”), gari ne na wadansu mutane, gari ne na wata kabila (don haka akwai kabilanci a cikin garin), gari ne wanda duk abin da ka taba sai an yi maka gori a kansa. To wadannan mutane ya za a yi su yarda sabon abu ya shigo cikinsu?

  • Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)
  • Muna Murna Da Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (1)

Amma mutanen Madina su kuwa mutane ne wadanda suke neman duk wani wanda zai kawo masu ci gaba a kan ya zo ya zauna a cikinsu. Sunan Garin Madina “Yathrib”, kabilu biyu ne kawai a ciki; (i) Ausu da (ii) Khazraj, sai Yahudawa; Kainuka’a da Nadhiru da Kuraizah a gefensu, amma kuma Kakarsu gaba daya guda daya ce sunanta Kailata. To Manzon Allah (SAW) sai ya ga ga wuri, amma kuma ko inda ya zauna har yanzu dai akwai kabilu, Ausu da Khazraj, akwai yiwuwar fitina, sai Manzo (SAW) ya canza mata suna daga Yathrib zuwa “Madinah” (watau Birni), su kansu kabilun ma sai ya canza masu suna suka koma “Ansaru” (ma’ana mataimaka). Yanzu da Ausu da Khazraj da duk sauran sunansa daya, watau “Ansaru”, su zauna lafiya da addini daya, gari daya.

ADVERTISEMENT

Amma da Manzon Allah SAW ya bar su da sunan Ausu da Khazraj din nan ba za a taba zama lafiya ba. To wannan irin wayewa da Manzon Allah SAW ya nuna to haka addinin yake. Babban misali shi ne irin yadda muka hada addini da al’adar garuruwansu na Nijeriya, za ka ga da ka je Abuja komai ya fita daban, ta hanyar ‘yanci da walwala da sakewa a addini, akasin a tsofaffin biranenmu wanda da ka yi abu na addini amma bako masalan, za ka ji tsofaffi sun fara fadar: “kai dan gidan waye a garin nan? Waye babanka a garin nan?”

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya zo mana da wayewa da birnantaka, ya zo mana da Kur’ani, wanda yake nuna mana birnantaka shi ma, ya yarda da zaman kabilu a waje daya, ya yarda da zaman addinai a waje daya, ya yarda da zaman littafai kala-kala (kamar yadda muka kawo a tafsirai), ya yadda da zaman jama’a kala-kala; amma dai a zama ana karkashin tsarin mulki (constitution) guda daya. Shi kuwa tsarin mulki (watau constitution) ba addini ko kabila yake dubawa ba, yana duba zaman lafiyar ‘ya`yan wannan kasa ne. Wannan kuwa rahama ce, ita rahama idan ta zo babu ruwanta da addini ko kabila ko al’ada, wannan alheri ne. Muna addu’ar Allah ya dawo da dukkan Musulmi a kan hanyar Manzon Allah (SAW), mu zama rayayyu, mu guji fitintinu, mu bi wannan littafi na Manzon Allah (SAW) da ya wayar da kan duniya baki daya, ya sa musulunci ya keta duniya tun daga Sindu, watau Pakistan (duk da cewar daga baya ya shiga har Hindu, watau Indiya, da Jakarta, da sauransu) sai da ya kai har Danja (Morocco), sai da ya kai har Faransa, cikin wayewa.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Duk wani bangaren wayewa da kimiyya da fasaha za ka ga asali malaman Musulunci ne suka zo da shi, babu lokaci isasshe da mun kawo misalai masu yawa. yana daga cikin wayewar nan: tashi a sama zuwa duniyar wata, da duk “technology” din nan na zamani, harkar zane-zane, kade-kade, bushe-bushe. Amma duk aka kwashe wadannan aka bar mu sai dai halal da haram kawai! Su ma din an hana ma halal din gurbin ta, ba mu da wata magana sai dai haram! Da a ce malamai biyar za su taru, to za ka ga ba za su kago komai ba sai haram. Amma sauran malaman kasar Turai kuwa da zarar sun hadu sai ka ga sun kago wata sabuwar kira, su kuma mutanenmu sai dai ka ji sun ce “ai duk wannan duniya ce suke kagowa!”. To wa ya kai ka lahirar in ba duniyar ba? Yanzu ba don sun kago jirgin sama ba waye zai kai ka Hajji da Umrah cikin sauri?

Jama’a mu waye, saboda addininmu wayayye ne, Annabinmu wayayye ne, Kur’aninmu wayayye ne. Abin da yasa bama fadar wadansu abubuwan ma saboda raunana. Amma yanzu an waye duka gaba daya, wayar salular nan taka babban malami ce, ka tambayi “Google” ko mene ne za ta zo maka da labarin komai, duk wasu abubuwa da aka canza a addinin nan siyasa ce ta jawo aka canza shi, amma asalinsa lafiya kalau yake, duk wayewa ce da sauki da ci gaba, idan ka duba Al-kur’ani duk haka za ka gani.

Mu yi murna dai jama’a, kuma yana ga kan malamai na addini, su rika binciken gaskiya duk inda take, su rika binciken ilimi, mu koma ma manyan littafai, littafan da aka yi tun daga wajen karni na biyu, abubuwa sun faru da yawa wanda ba za su fadu ba, amma ga littafai na karni na biyu tun daga nan aka fara, malamai sun yi kokari, mu rika koma ma wadannan da wayewa da fahimta da kwakwalwa irin ta zamani ba irin ta wancan zamani ba, saboda duk abin da suka yi mai kyau ne, amma kuma an ci gaba, Allah shi ne zamani, Allah ya kawo wayewa, Allah ya kawo wadanda Annabi da kansa ya fadi zuwan zamaninsu da wayewarsu. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya ce “Karshen zamani ilImi zai yawaita”. Amma ikon Allah, galibin littafan da muke karantawa suna nuni da karshen zamani ilimi zai kare. Ka san babu wanda ya isa ya ce ilimi ya kare a yanzu, yanzu ilmi ya fara ma! Ka ga ashe wannan hadisi da Manzon Allah ya ce karshen zamani ilimi zai yawaita gaskiya ne kuma shi ne daga Manzon Allah (SAW), ba littafan malaman nan ba.

Don Allah malamai ku duba manyan littafai, ku zama masu amana ta ilimi (amana ilmiyya), ku zamanto masu hango ma al’umma ci gaba, da wayewa, ba masu dakikantar da al’umma ba, ku zamanto jagorori a cikin duk abin da za ku fada, da duk abinda za ku rubuta, da duk littafin da za ku yi, duk abin da kuka yi zai same ku a cikin kabarinku. Kar don wani abu bai dace da jama’arku ba ku ce karya ne, ko ku ki yarda da shi, ko bai dace da kabilarku ba, ko bai dace da kungiyar da kake bi ba. Duk wadannan sun shiga cikin addini sun lalata shi, ba laifi rike akidu da maz’habobi amma kuma ya kamata a dauki abubuwan da suke ciki masu kyau a zubar da abubuwan da ba su da kyau. Zamani ya yi fa wanda in dai ba mu gyara ba Allah zai gyara mana fa! Manzon Allah (SAW) ya yi gaskiya, mai gaskiya ne abin gaskatawa, ya isar da sako kuma ya isar da amana. Mu zama masu adalci; asali shi ne wanda zai yi hukunci a tsakanina jama’a biyu kuma ya yi adalci a tsakaninsu. Kisdu kuma shi ne a tsakanin mutum biyu kawai, misali kamar tsakanin mai awo da wanda ake wa awon.

Muna taya dukkan al’ummar musulmi murnar ganin wannan lokaci mai tarihi na cikar Manzon Allah (SAW) shekara 1500 da haihuwa. Alhamdu Lillah!

Maulidin
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Maulidin
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Me Ake Nufi Da Ado? 

Me Ake Nufi Da Ado? 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.