Tawagar hafsoshin sojojin Afirka kusan 100 matasa da masu matsakaitan shekaru sun fara ziyararsu a kasar Sin a yau Talata, bisa gayyatar da ma’aikatar tsaron kasar Sin ta yi musu.
Tawagar wadda ke wakiltar kasashen Afirka sama da 40 da suka hada da Masar da Mozambique da Tanzaniya da kuma Kenya, ta shirya gudanar da ziyara zuwa wuraren da suka hada da Beijing, Changsha, Shaoshan da sauran wurare da dama domin yin musaya, wanda za a kammala a ranar 15 ga watan Mayu.
A cewar ma’aikatar tsaron kasar Sin, ziyarar wadda ita ce irinta ta hudu, na da nufin fassara yarjejeniyoyin da aka cimma a taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing zuwa ayyuka na zahiri da zurfafa dadadden zumunci tsakanin sojojin Sin da Afirka. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp