• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 month ago
in Daga Birnin Sin
0
Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan aukuwar wata girgizar kasa mai karfin gaske jiya Juma’a a kasar, da sanyin safiyar yau Asabar, agogon Myanmar din, tawagar ma’aikatan ceto ta lardin Yunnan na kasar Sin, mai mambobi 37, ta isa birnin Yangon na kasar. Tawagar wadda ta kasance tawagar ceto ta kasa da kasa ta farko da ta isa Myanmar, na dauke da na’urorin agajin gaggawa guda 112, ciki har da na’urorin tantance mai rai, da na gargadin girgizar kasa, da na’urorin sadarwa masu amfani da tauraron dan adam, da na’urori masu tashi sama. 

Kafin haka, wani mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin ta damu matuka da bala’in girgizar kasar da ta afku a kasar Myanmar, inda ya jajenta wa al’ummar kasar. Ya ce kasar Sin tana son ba da agajin gaggawa da taimakon jin kai ga yankunan da bala’in ya rutsa da su gwargwadon karfinta, kuma bisa bukatun kasar Myanmar. Bugu da kari, ya ce Sinawa za su kasance tare da al’ummar Myanmar wajen yaki da bala’in da kuma shawo kan matsalolin da ake fuskanta.

  • Shugaba Xi Ya Jajantawa Shugaban Myanmar Game Da Girgizar Kasar Da Ta Auku
  • Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Ban da haka, kasar Sin ta yanke shawarar samar wa Myanmar tallafin jin kai na yuan miliyan 100, kwatankwacin dala miliyan 13.9, domin taimakawa wajen saukaka radadin ibtila’in girgizar kasa da ta aukawa kasar. Kakakin hukumar raya kasashe ta kasar Sin Li Ming ne ya bayyana haka a yau Asabar. Ya kara da cewa, bisa bukatar gwamnatin Myanmar, Sin za ta tura tawagogi 2 na ma’aikatan ceto tare da samar da tantuna da barguna da kayayyakin kiwon lafiya na gaggawa da abinci da ruwan sha, wadanda su ake mutukar bukata a yankunan da ibtila’in ya shafa.

Da tsakar ranar jiya Juma’a, agogon kasar Myanmar, girgizar kasa mai karfin maki 7.9 ta afku a tsakiyar kasar, bala’in da ya sanya dimbin yankunan kasar shiga cikin dokar ta-baci. A cewar kafofin yada labaru na Myanmar, bala’in ya riga ya haddasa mutuwar mutane 1002 tare da jikkata wasu 2376 a cikin kasar, kuma adadin wadanda suka mutu ka iya karuwa. (Bello Wang/Fa’iza Muhammad Mustapha)

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanonin Kasashen Waje Na Da Imani Kan Ingancin Kasuwar Kasar Sin 

Next Post

Mu Yi Riƙo Da Kyawawan Ɗabi’u Har Bayan Ramadan – Sudais

Related

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

2 hours ago
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

2 hours ago
Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

18 hours ago
He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala
Daga Birnin Sin

He Lifeng Ya Gana Da Babbar Jami’ar WTO Ngozi Okonjo-Iweala

20 hours ago
Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu

21 hours ago
Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Latin Amurka Na Kara Samun Karbuwa Tsakanin Jama’a

23 hours ago
Next Post
Mu Yi Riƙo Da Kyawawan Ɗabi’u Har Bayan Ramadan – Sudais

Mu Yi Riƙo Da Kyawawan Ɗabi'u Har Bayan Ramadan - Sudais

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamna Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya Gargaɗi Magoya Bayansa

May 13, 2025
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano

May 13, 2025
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

May 13, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

May 13, 2025
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

May 13, 2025
Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.