ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar Ma’aikatan Ceto Ta Kasar Sin Ta Isa Birnin Yangon Na Kasar Myanmar 

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Myanmar

Bayan aukuwar wata girgizar kasa mai karfin gaske jiya Juma’a a kasar, da sanyin safiyar yau Asabar, agogon Myanmar din, tawagar ma’aikatan ceto ta lardin Yunnan na kasar Sin, mai mambobi 37, ta isa birnin Yangon na kasar. Tawagar wadda ta kasance tawagar ceto ta kasa da kasa ta farko da ta isa Myanmar, na dauke da na’urorin agajin gaggawa guda 112, ciki har da na’urorin tantance mai rai, da na gargadin girgizar kasa, da na’urorin sadarwa masu amfani da tauraron dan adam, da na’urori masu tashi sama. 

Kafin haka, wani mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana cewa, kasar Sin ta damu matuka da bala’in girgizar kasar da ta afku a kasar Myanmar, inda ya jajenta wa al’ummar kasar. Ya ce kasar Sin tana son ba da agajin gaggawa da taimakon jin kai ga yankunan da bala’in ya rutsa da su gwargwadon karfinta, kuma bisa bukatun kasar Myanmar. Bugu da kari, ya ce Sinawa za su kasance tare da al’ummar Myanmar wajen yaki da bala’in da kuma shawo kan matsalolin da ake fuskanta.

  • Shugaba Xi Ya Jajantawa Shugaban Myanmar Game Da Girgizar Kasar Da Ta Auku
  • Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Ban da haka, kasar Sin ta yanke shawarar samar wa Myanmar tallafin jin kai na yuan miliyan 100, kwatankwacin dala miliyan 13.9, domin taimakawa wajen saukaka radadin ibtila’in girgizar kasa da ta aukawa kasar. Kakakin hukumar raya kasashe ta kasar Sin Li Ming ne ya bayyana haka a yau Asabar. Ya kara da cewa, bisa bukatar gwamnatin Myanmar, Sin za ta tura tawagogi 2 na ma’aikatan ceto tare da samar da tantuna da barguna da kayayyakin kiwon lafiya na gaggawa da abinci da ruwan sha, wadanda su ake mutukar bukata a yankunan da ibtila’in ya shafa.

ADVERTISEMENT

Da tsakar ranar jiya Juma’a, agogon kasar Myanmar, girgizar kasa mai karfin maki 7.9 ta afku a tsakiyar kasar, bala’in da ya sanya dimbin yankunan kasar shiga cikin dokar ta-baci. A cewar kafofin yada labaru na Myanmar, bala’in ya riga ya haddasa mutuwar mutane 1002 tare da jikkata wasu 2376 a cikin kasar, kuma adadin wadanda suka mutu ka iya karuwa. (Bello Wang/Fa’iza Muhammad Mustapha)

 

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
Mu Yi Riƙo Da Kyawawan Ɗabi’u Har Bayan Ramadan – Sudais

Mu Yi Riƙo Da Kyawawan Ɗabi'u Har Bayan Ramadan - Sudais

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.