• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ba Zai Yi Murabus Ba, inji Ministan Yaɗa Labarai 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Ministan Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kiran da Ƙungiyar Gwamnonin PDP ta yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ya yi murabus ba komai ba ne illa wani yunƙuri na karkatar da hankalin jama’a daga mutanen da ya kamata su shagaltu da tallafa wa ƙoƙarin shugaban ƙasa na kawo wa al’ummar Nijeriya agajin gyaran tattalin arziki.

A cewarsa, bai kamata PDP da gwamnonin ta su riƙa nema, ta hanyar tsoratarwa, abin da su ka kasa cimmawa ta hanyar dimokiraɗiyya tun cikin 2015.

  • Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayyana A Ofishin Hukumar EFCC Da Ke Jihar
  • Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan aikin jarida, Rabi’u Ibrahim, ya bayar, Idris ya ce: “Bai kamata waɗanda su ka gaza kawo sauyi a lokacin da su ka samu dama mai tsawo ba su nemi katsewa ko karkatar da hankalin masu aiki kan manufar shugaban ƙasa da ‘yan Nijeriya su ka zaɓe su don aiwatarwa ba.

“Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, tun da aka kafa ta, ta ba da tallafin kuɗi ga dukkan gwamnatocin jihohi, ba tare da la’akari da ɓangaranci ba.

“Kazalika, cire tallafin man fetur, wanda aka yi ba zato ba tsammani, ya na ɗaya daga cikin manyan ginshiƙan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, wato don ya ƙara kuɗaɗen shiga na ɗaukacin jihohi, ciki har da jihohin PDP. Wanda aka ba da yawa, ana sa ran samun da yawa daga wurin shi.”

Labarai Masu Nasaba

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

Ministan ya ce, “Shugaban Ƙasa da gwamnatin sa sun amince da ayyukan da ba a kammala ba na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar mu da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara, ta hanyar shirye-shiryen da su ka mayar da hankali kan manyan ababen more rayuwa, walwala da jin daɗin jama’a, da ba da fifiko wajen samar da kayan aiki da kyautata wa sojoji da hukumomin tsaro, da kuma maido da Nijeriya turbar matsayi mai mahimmanci a tsakanin ƙasashe.”

Ya yi nuni da cewa tun daga shekarar 2014/2015 aka kawo ƙarshen Boko Haram da masu alaƙa da su, kuma a halin yanzu ana samun irin wannan gagarumar nasarar a kan ‘yan bindiga da sauran miyagun mutane.

A cewar sa, ‘yan Nijeriya dai ba su manta da cewa gwamnatin APC ce ta kawar da naƙasu da dama da gwamnatin PDP ta bari a baya ba, kamar neman tallafin man fetur da ‘yan kasuwar man fetur ke yi, da dawo da kuɗaɗen Paris Club, biyan fansho da ba a biya ba, da kuɗaɗen sallama daga aiki, da basussukan albashi da ake bin kashi daban-daban na ’yan fansho daga kamfanoni mallakar gwamnati da aka sayar da kuma waɗanda ake da su a yanzu.

Ya ce: “Manyan sauye-sauye a ɓangaren man fetur da PDP ta dinga tallatawa na tsawon shekaru amma ta kasa cimmawa – ƙaddamar da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIB), sababbin matatun mai, da kuma sake fasalin waɗanda ake da su, da sauran su – su ne ainihin abubuwan da jam’iyya mai mulki ta APC ta yi.

“Dukkan waɗannan an yi su ne ba tare da samun ribar man fetur da gwamnatin PDP ta ci a tsawon lokacin da ta ke kan karagar mulki ba, sannan kuma a lokacin annobar COVID-19.

“Dole ne mu ci gaba da bayyana waɗannan hujjoji domin ’yan Nijeriya su san daga inda mu ke, kuma su yaba da abin da ake yi.

“Shugaba Tinubu ba zai taɓa gajiyawa da ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a halin yanzu ba. Ba zai yi watsi da nauyin da ke kan sa ba, da jajircewa zai ci gaba da kokawa da shawo kan ƙalubalen da ke gaban sa, tare da aza harsashi mai ɗorewa ga sabuwar Nijeriya da ke tasowa.

“Har ila yau, ba zai ce bai san raɗaɗin sauye-sauyen da ake ci gaba da yi ba, ya kuma yi amfani da duk wata dama da za ta samu wajen tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa raɗaɗin sauye-sauyen ya ta’allaƙa ne da samar da arziki mai ɗorewa da cigaban ƙasa.

“Ga gwamnonin PDP, bari mu sake nanata cewa: Wannan ba lokacin da za a raba hankali ba ne. Lokaci ya yi da za a yi shirin aiki, don tallafawa da cika aikin Shugaban Ƙasa da gwamnatin sa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dambarwar siyasar NijeriyaDurkushewar darajar NairaMinistan Yaɗa LabaraiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Karfi Ce Ta Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

Next Post

Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

Related

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

7 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

8 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

9 hours ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

10 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

11 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.