• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ba Zai Yi Murabus Ba, inji Ministan Yaɗa Labarai 

by Sulaiman
2 years ago
Ministan Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kiran da Ƙungiyar Gwamnonin PDP ta yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ya yi murabus ba komai ba ne illa wani yunƙuri na karkatar da hankalin jama’a daga mutanen da ya kamata su shagaltu da tallafa wa ƙoƙarin shugaban ƙasa na kawo wa al’ummar Nijeriya agajin gyaran tattalin arziki.

A cewarsa, bai kamata PDP da gwamnonin ta su riƙa nema, ta hanyar tsoratarwa, abin da su ka kasa cimmawa ta hanyar dimokiraɗiyya tun cikin 2015.

  • Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayyana A Ofishin Hukumar EFCC Da Ke Jihar
  • Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan aikin jarida, Rabi’u Ibrahim, ya bayar, Idris ya ce: “Bai kamata waɗanda su ka gaza kawo sauyi a lokacin da su ka samu dama mai tsawo ba su nemi katsewa ko karkatar da hankalin masu aiki kan manufar shugaban ƙasa da ‘yan Nijeriya su ka zaɓe su don aiwatarwa ba.

“Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, tun da aka kafa ta, ta ba da tallafin kuɗi ga dukkan gwamnatocin jihohi, ba tare da la’akari da ɓangaranci ba.

“Kazalika, cire tallafin man fetur, wanda aka yi ba zato ba tsammani, ya na ɗaya daga cikin manyan ginshiƙan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, wato don ya ƙara kuɗaɗen shiga na ɗaukacin jihohi, ciki har da jihohin PDP. Wanda aka ba da yawa, ana sa ran samun da yawa daga wurin shi.”

LABARAI MASU NASABA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ministan ya ce, “Shugaban Ƙasa da gwamnatin sa sun amince da ayyukan da ba a kammala ba na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar mu da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara, ta hanyar shirye-shiryen da su ka mayar da hankali kan manyan ababen more rayuwa, walwala da jin daɗin jama’a, da ba da fifiko wajen samar da kayan aiki da kyautata wa sojoji da hukumomin tsaro, da kuma maido da Nijeriya turbar matsayi mai mahimmanci a tsakanin ƙasashe.”

Ya yi nuni da cewa tun daga shekarar 2014/2015 aka kawo ƙarshen Boko Haram da masu alaƙa da su, kuma a halin yanzu ana samun irin wannan gagarumar nasarar a kan ‘yan bindiga da sauran miyagun mutane.

A cewar sa, ‘yan Nijeriya dai ba su manta da cewa gwamnatin APC ce ta kawar da naƙasu da dama da gwamnatin PDP ta bari a baya ba, kamar neman tallafin man fetur da ‘yan kasuwar man fetur ke yi, da dawo da kuɗaɗen Paris Club, biyan fansho da ba a biya ba, da kuɗaɗen sallama daga aiki, da basussukan albashi da ake bin kashi daban-daban na ’yan fansho daga kamfanoni mallakar gwamnati da aka sayar da kuma waɗanda ake da su a yanzu.

Ya ce: “Manyan sauye-sauye a ɓangaren man fetur da PDP ta dinga tallatawa na tsawon shekaru amma ta kasa cimmawa – ƙaddamar da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIB), sababbin matatun mai, da kuma sake fasalin waɗanda ake da su, da sauran su – su ne ainihin abubuwan da jam’iyya mai mulki ta APC ta yi.

“Dukkan waɗannan an yi su ne ba tare da samun ribar man fetur da gwamnatin PDP ta ci a tsawon lokacin da ta ke kan karagar mulki ba, sannan kuma a lokacin annobar COVID-19.

“Dole ne mu ci gaba da bayyana waɗannan hujjoji domin ’yan Nijeriya su san daga inda mu ke, kuma su yaba da abin da ake yi.

“Shugaba Tinubu ba zai taɓa gajiyawa da ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a halin yanzu ba. Ba zai yi watsi da nauyin da ke kan sa ba, da jajircewa zai ci gaba da kokawa da shawo kan ƙalubalen da ke gaban sa, tare da aza harsashi mai ɗorewa ga sabuwar Nijeriya da ke tasowa.

“Har ila yau, ba zai ce bai san raɗaɗin sauye-sauyen da ake ci gaba da yi ba, ya kuma yi amfani da duk wata dama da za ta samu wajen tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa raɗaɗin sauye-sauyen ya ta’allaƙa ne da samar da arziki mai ɗorewa da cigaban ƙasa.

“Ga gwamnonin PDP, bari mu sake nanata cewa: Wannan ba lokacin da za a raba hankali ba ne. Lokaci ya yi da za a yi shirin aiki, don tallafawa da cika aikin Shugaban Ƙasa da gwamnatin sa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC
Labarai

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi
Manyan Labarai

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Next Post
Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.