ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ba Zai Yi Murabus Ba, inji Ministan Yaɗa Labarai 

by Sulaiman
2 years ago
Ministan Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa kiran da Ƙungiyar Gwamnonin PDP ta yi wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu na ya yi murabus ba komai ba ne illa wani yunƙuri na karkatar da hankalin jama’a daga mutanen da ya kamata su shagaltu da tallafa wa ƙoƙarin shugaban ƙasa na kawo wa al’ummar Nijeriya agajin gyaran tattalin arziki.

A cewarsa, bai kamata PDP da gwamnonin ta su riƙa nema, ta hanyar tsoratarwa, abin da su ka kasa cimmawa ta hanyar dimokiraɗiyya tun cikin 2015.

  • Tsohon Gwamnan Jihar Kwara Ya Bayyana A Ofishin Hukumar EFCC Da Ke Jihar
  • Dambarwar Shari’ar Murja Kunya: Gwamnatin Kano Ta Musanta Yin Katsalandan Kan Shari’ar

A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan aikin jarida, Rabi’u Ibrahim, ya bayar, Idris ya ce: “Bai kamata waɗanda su ka gaza kawo sauyi a lokacin da su ka samu dama mai tsawo ba su nemi katsewa ko karkatar da hankalin masu aiki kan manufar shugaban ƙasa da ‘yan Nijeriya su ka zaɓe su don aiwatarwa ba.

ADVERTISEMENT

“Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, tun da aka kafa ta, ta ba da tallafin kuɗi ga dukkan gwamnatocin jihohi, ba tare da la’akari da ɓangaranci ba.

“Kazalika, cire tallafin man fetur, wanda aka yi ba zato ba tsammani, ya na ɗaya daga cikin manyan ginshiƙan yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, wato don ya ƙara kuɗaɗen shiga na ɗaukacin jihohi, ciki har da jihohin PDP. Wanda aka ba da yawa, ana sa ran samun da yawa daga wurin shi.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Ministan ya ce, “Shugaban Ƙasa da gwamnatin sa sun amince da ayyukan da ba a kammala ba na farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasar mu da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta fara, ta hanyar shirye-shiryen da su ka mayar da hankali kan manyan ababen more rayuwa, walwala da jin daɗin jama’a, da ba da fifiko wajen samar da kayan aiki da kyautata wa sojoji da hukumomin tsaro, da kuma maido da Nijeriya turbar matsayi mai mahimmanci a tsakanin ƙasashe.”

Ya yi nuni da cewa tun daga shekarar 2014/2015 aka kawo ƙarshen Boko Haram da masu alaƙa da su, kuma a halin yanzu ana samun irin wannan gagarumar nasarar a kan ‘yan bindiga da sauran miyagun mutane.

A cewar sa, ‘yan Nijeriya dai ba su manta da cewa gwamnatin APC ce ta kawar da naƙasu da dama da gwamnatin PDP ta bari a baya ba, kamar neman tallafin man fetur da ‘yan kasuwar man fetur ke yi, da dawo da kuɗaɗen Paris Club, biyan fansho da ba a biya ba, da kuɗaɗen sallama daga aiki, da basussukan albashi da ake bin kashi daban-daban na ’yan fansho daga kamfanoni mallakar gwamnati da aka sayar da kuma waɗanda ake da su a yanzu.

Ya ce: “Manyan sauye-sauye a ɓangaren man fetur da PDP ta dinga tallatawa na tsawon shekaru amma ta kasa cimmawa – ƙaddamar da Dokar Masana’antar Man Fetur (PIB), sababbin matatun mai, da kuma sake fasalin waɗanda ake da su, da sauran su – su ne ainihin abubuwan da jam’iyya mai mulki ta APC ta yi.

“Dukkan waɗannan an yi su ne ba tare da samun ribar man fetur da gwamnatin PDP ta ci a tsawon lokacin da ta ke kan karagar mulki ba, sannan kuma a lokacin annobar COVID-19.

“Dole ne mu ci gaba da bayyana waɗannan hujjoji domin ’yan Nijeriya su san daga inda mu ke, kuma su yaba da abin da ake yi.

“Shugaba Tinubu ba zai taɓa gajiyawa da ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a halin yanzu ba. Ba zai yi watsi da nauyin da ke kan sa ba, da jajircewa zai ci gaba da kokawa da shawo kan ƙalubalen da ke gaban sa, tare da aza harsashi mai ɗorewa ga sabuwar Nijeriya da ke tasowa.

“Har ila yau, ba zai ce bai san raɗaɗin sauye-sauyen da ake ci gaba da yi ba, ya kuma yi amfani da duk wata dama da za ta samu wajen tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa raɗaɗin sauye-sauyen ya ta’allaƙa ne da samar da arziki mai ɗorewa da cigaban ƙasa.

“Ga gwamnonin PDP, bari mu sake nanata cewa: Wannan ba lokacin da za a raba hankali ba ne. Lokaci ya yi da za a yi shirin aiki, don tallafawa da cika aikin Shugaban Ƙasa da gwamnatin sa.”

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

Tsadar Rayuwa: An Ci Gaba Da Gudanar Da Zanga-zanga A Ibadan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.