Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da kashe Naira biliyan 80 don sake gina madatsar ruwa ta Alau a jihar Borno.
Ministan albarkatun ruwa da tsaftar mahalli, Joseph Utsev ne ya bayyana haka a ranar Talata bayan kammala taron majalisar zartarwa ta tarayya karo na biyu wanda shugaba Tinubu ya jagoranta a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
- Dakarun Sojin Sama Na PLA Sun Yi Shawagin Sintiri A Tsibirin Huangyan
- ‘Yan Bindiga Sun Harbe Mutum 2, Sun Yi Garkuwa Da Wasu 5 A Kaduna.
Utsev ya ce, gwamnatin jihar Borno na hada kai da gwamnatin tarayya domin fara aikin da aka shirya gudanarwa cikin watanni 24 masu zuwa.
Ministan ya kara da cewa, za a kaddamar da kashin farko na gyaran madatsar ruwan a tsakanin watan Fabrairu zuwa Yulin 2025.
Ya kuma kara jaddada muhimmancin wannan aiki na tabbatar da cewa ba a samu ambaliyar ruwa a jihar Borno a shekarar 2025 ba.