• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ceto Dimokuradiyyar Nijeriya Bisa Kin Katsalandan A Shari’ar Gwamnoni – Kabiru Marafa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Ko-odinetan yakin neman zaben Tinubu a Zamfara a zaben da ya gabata, Sanata Kabiru Marafa ya bayyana cewa rashin katsalandan Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu a shari’o’in zaben gwamnoni a kotun koli ya yi matukar ceto dimokuradiyyar kasar nan da kuma farfado da bangaren shari’a.

A ranar Juma’a da ta gabata ce, kotun koli ta raba gardama a zaben gwamnoni guda 8, inda ta tabbatar da nasarar gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, gwamnan Jihar Ebonyi, Francis Nwifuru, gwamnan Jihar Abiya, Aled Otti da kuma gwamnan Jihar Kuros Riba, Bassey Otu.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Nijeriya Na Fatan Samun Karin Masu Zuba Jari A Taron Kasuwanci Na Duniya

 Marafa ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya bayyana cewa Shugaba Tinubu da alkalan kotun koli sun cancanji yabo a wurin ‘yan Nijeriya, saboda sun tabbatar da abun da ‘yan Nijeriya suka zaba.

Ya yaba wa shugaban kasa na kin yin katsalandan, musamman ma a shari’ar gwamnan Jihar Kano wanda ya samu matsin lamba daga magoya bayan jam’iyyarsa.

Marafa ya ce, “Abin farin ciki ne yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu bai tsoma baki a hukuncin kotun koli ba, haka ya ceci dimokuradiyyar kasar tare da hana sake faruwan abin da ya auko a shekarar 1983.”

Da yake jinjina wa alkalan kotun kolin, Sanata Marafa ya ce sun cika abin da talakawan Nijeriya ke bukata, inda ya ce sun sanya kasar cikin alfahari.

Ya tuno da irin wannan lamari da ya faru zaben 2019, inda a lokacin yake fafatukan neman tikitin takarar gwamnan Zamfara a karkashin jam’iyyar.

Ya ce, “Na yi adawa na nuna rashin amincewa da yadda zaben fid da gwani wajen tsayar da ‘yan takara da Abdulaziz Yari ya samu nasara, inda bangaren shari’a ya tsaya tsayin daka wajen zartar da hukunci da ya bai wa jam’iyyar adawa ta PDP a jihar baki daya.

“Dole ne a bar bangaren shari’a su kasance masu gaskiya da adalci idan ‘yan siyasa suna son dimokuradiyya ta dore a kasar nan.”

Marafa ya bukaci gwamnonin takwas da su kasance masu kankan da kai da adalci wajen tafiyar da mulki a jihohinsu.

Ya taya gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal murna tare da jawo hankalinsa wajen yin aiki domin cika amincewar da al’ummar jihar suka yi masa.

Marafa ya ce, “A saboda haka, ina kira ga gwamnan jiharmu ta Zamfara da ya hada kai da mai girma Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Sanata Kashim Shettima da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya da tsaro da ake bukata a Jihar Zamfara. Zaman lafiya shi ne abin da jama’armu ke fata ba komai ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Kamaru Sun Yi Alkawarin Kara Samun Sabbin Nasarori A Hadin Gwiwar Dake Tsakaninsu

Next Post

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Related

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

11 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

1 day ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

1 day ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

1 day ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Next Post
Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

Yadda Za Ku Inganta Rayuwarku A 2024 A Kimiyyance

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.