• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Hadu Da Shugabannin Duniya A Faransa Don Tunkarar Matsalar Talauci Da Basuka

Macron, Guterres Sun Bukaci A Samar Da Sabon Tsarin Hada-hadar Kudi Na Duniya

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Hadu Da Shugabannin Duniya A Faransa Don Tunkarar Matsalar Talauci Da Basuka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis ya hadu tare da sauran shugabannin kasashen duniya a Paris-France a wajen babban taron kan yarjejeniyar kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na duniya, wacce kai tsaye hakan zai taimaka wajen rage kaifin talauci, shawo kan basuka ko sokewa da kuma la’akari da kananun kasashen da annobar Korona ta raunata.

Tinubu ya halarci wurin taron da ke Palais Brongniart, da karfe 8.59 am agogon Nijeriya domin halartar bude taron sabon tsarin hada-hadar kudi na duniya, inda ya samu tarba daga ministan Faransa da ke kula da harkokin kasashen waje, Catherine Colonna.

  • Li Qiang: Alakar Kasashen Sin Da Faransa Tana Da Ma’ana A Duniya.

A sanarwar manema labarai, Dele Alake, da yake marabtar bakin, shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce, babban taron na da manufar hada tunani waje guda ne domin samar da sabon tsarin hada-hadar kudi na duniya wanda hakan zai taimaka sosai wa kasashe masu tasowa wajen sauyin makamashi, yaki da talauci da fatara, tare da muunta ‘yancin kowace qasa domin kyautata rayuwa.

Shugaban na Faransa, ya kara cewa kasashen Afrika suna kan gaba wajen fuskantar manyan matsaloli, tare da tulin basuka da suke janyo koma baya ga cigaban kasashen, don haka ya ce, taron zai taimaka wajen fuskantar irin wadannan matsalolin domin neman mafiya.

“Annobar Korona ta janyo wahala da mawuyacin yanayi matuka, yanzu muna fuskatar yakin Ukraine da ya janyo babban matsala ga tattalin arziki,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Macron ya shaida wa shugabannin kasashen 50, akwai bukatar sake zurfin nazari wajen ganin yadda za a tafiyar da kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyi domin ganin kowani bangare na amfanuwa da juna tare da maida hankali kan masu rauni don a tafi tare.

Ya ce, babban matsalar fatara da talauci tabbas na bukatar hada karfi da karfe tare da fito da muhimman dabaru da hikomin shawo kansa, “Ya kamata dukkaninmu mu yarda cewa babu wata kasa da za ta iya magance matsalar fatara ita kadai,” ya kara.

Macron ya ce, tsarin da za a fitar din zai hada da masu ruwa da tsari a kasashen, shiyoyi, shigo da kamfanoni da cibiyoyi masu zaman kasnu musamman irin International Monetary Fund da bankin duniya World Bank domin fito da matakan kawo gyara.

Ya sake nanata cewa kamfanoni masu zaman kansu na da gayar muhimmanci a janyo su jika wajen fitar da sabon tsari domin fuskantar cigaba mai ma’ana, kazalika, ya ce, a irin lokacin da ake neman kawo sauyi ga sashin hada-hadar kudade akwai wasu fannonin da suke bukatar kula da suka hada da kiwon lafiya, ilimi da wadatar abinci.

A madadin kasashen Afrika kuwa, shugaban jamhuriyar Nijar, Mohammed Bazoum, ya ce, dole sabon yarjejeniyar ya kasance cikin hanzari da muhimmanci ga Afrika sannan, tsarin da za a fitar din a yi wajen tsage gaskiya domin tabbatar da a zahirance kasashe masu tasowa sun amfana a matsayin abokan jere.

Bazoum ya ce, matsalolin talauci da kwararowar hamada sun addabi kasashensu, da ke shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a nahiyar.

A cewarsa, “A Afirka muna bukatar taimako wajen shimfida ayyuka, kiwon lafiya, wadatar abinci da ilimi.”

Sakatare janar na majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres, ya shaida wa shugabannin cewa taron na da bukatar yin tsarin da kowa zai ji a jikinsa ya dace a aiwatar ba wai a zana a watse ba kawai.

Guterres ya ce, kasashe da dama har yanzu suna fama da radadin illar da annobar Korona ta musu da kuma na dumamar yanayi, da yakin Ukraine da dai sauransu.

Guterres ya kara da cewa, kasashen Afirka ba su samu wadataccen hanyoyin biyan basukan da suke makale a wuyayensu, da hakan ke barazanar cewa nan gaba al’ummar da ke tasowa za su iya shiga mawuyacin hali sakamakon wannan tulin basukan.

Ya ce, tsarin yarjejeniyar kudin na da bukatar ya duba wadannan matsalolin ta yadda za a shigar cikin tsarin domin shawo kan tulin matsalolin da suke akwai, ya nuna damuwarsa kan basukan da ke kan kasashen Afrika, inda ya nuna hasken cewa ta hanyar kyakkyawar tsarin da aiki tukuru za a iya magance wasu daga cikin matsalolin.

Sakataren ya nuna bukatar da ke akwai ga shugabannin duniya da su hada hannu wajen fuskantar matsalolin da suke akwai domin samar da mafita da cigaban kasashe masamman masu tasowa.

Wani masani kan dumamar yanayi, Vanessa Nakate, da ya fito daga kasar Uganda, ya yi nemi a dan yi shiru domin jinjina wa marasa galihu da wadanda suke cikin mawuyacin hali a duniya, yana mai cewa karya al’kawura idan aka dauka na gurguntar da rayuwar mutane da dama a kasashe masu tasowa.

Tunin shugabannin da jagororin manyan kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyi suka tsunduma cikin taron domin nema hanyoyin da za a fitar da tsarin yarjejeniya da ake kyautata zaton zai taimaka sosai wajen rage talauci da basuka a kasashen duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Kasar Sin Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Ceto Yadda Ya Kamata Bayan Fashewar Da Ta Faru A Wani Gidan Cin Abinci

Next Post

Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

3 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

5 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

7 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

8 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

9 hours ago
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.