ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Hadu Da Shugabannin Duniya A Faransa Don Tunkarar Matsalar Talauci Da Basuka

Macron, Guterres Sun Bukaci A Samar Da Sabon Tsarin Hada-hadar Kudi Na Duniya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis ya hadu tare da sauran shugabannin kasashen duniya a Paris-France a wajen babban taron kan yarjejeniyar kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na duniya, wacce kai tsaye hakan zai taimaka wajen rage kaifin talauci, shawo kan basuka ko sokewa da kuma la’akari da kananun kasashen da annobar Korona ta raunata.

Tinubu ya halarci wurin taron da ke Palais Brongniart, da karfe 8.59 am agogon Nijeriya domin halartar bude taron sabon tsarin hada-hadar kudi na duniya, inda ya samu tarba daga ministan Faransa da ke kula da harkokin kasashen waje, Catherine Colonna.

  • Li Qiang: Alakar Kasashen Sin Da Faransa Tana Da Ma’ana A Duniya.

A sanarwar manema labarai, Dele Alake, da yake marabtar bakin, shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce, babban taron na da manufar hada tunani waje guda ne domin samar da sabon tsarin hada-hadar kudi na duniya wanda hakan zai taimaka sosai wa kasashe masu tasowa wajen sauyin makamashi, yaki da talauci da fatara, tare da muunta ‘yancin kowace qasa domin kyautata rayuwa.

ADVERTISEMENT

Shugaban na Faransa, ya kara cewa kasashen Afrika suna kan gaba wajen fuskantar manyan matsaloli, tare da tulin basuka da suke janyo koma baya ga cigaban kasashen, don haka ya ce, taron zai taimaka wajen fuskantar irin wadannan matsalolin domin neman mafiya.

“Annobar Korona ta janyo wahala da mawuyacin yanayi matuka, yanzu muna fuskatar yakin Ukraine da ya janyo babban matsala ga tattalin arziki,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Macron ya shaida wa shugabannin kasashen 50, akwai bukatar sake zurfin nazari wajen ganin yadda za a tafiyar da kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyi domin ganin kowani bangare na amfanuwa da juna tare da maida hankali kan masu rauni don a tafi tare.

Ya ce, babban matsalar fatara da talauci tabbas na bukatar hada karfi da karfe tare da fito da muhimman dabaru da hikomin shawo kansa, “Ya kamata dukkaninmu mu yarda cewa babu wata kasa da za ta iya magance matsalar fatara ita kadai,” ya kara.

Macron ya ce, tsarin da za a fitar din zai hada da masu ruwa da tsari a kasashen, shiyoyi, shigo da kamfanoni da cibiyoyi masu zaman kasnu musamman irin International Monetary Fund da bankin duniya World Bank domin fito da matakan kawo gyara.

Ya sake nanata cewa kamfanoni masu zaman kansu na da gayar muhimmanci a janyo su jika wajen fitar da sabon tsari domin fuskantar cigaba mai ma’ana, kazalika, ya ce, a irin lokacin da ake neman kawo sauyi ga sashin hada-hadar kudade akwai wasu fannonin da suke bukatar kula da suka hada da kiwon lafiya, ilimi da wadatar abinci.

A madadin kasashen Afrika kuwa, shugaban jamhuriyar Nijar, Mohammed Bazoum, ya ce, dole sabon yarjejeniyar ya kasance cikin hanzari da muhimmanci ga Afrika sannan, tsarin da za a fitar din a yi wajen tsage gaskiya domin tabbatar da a zahirance kasashe masu tasowa sun amfana a matsayin abokan jere.

Bazoum ya ce, matsalolin talauci da kwararowar hamada sun addabi kasashensu, da ke shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a nahiyar.

A cewarsa, “A Afirka muna bukatar taimako wajen shimfida ayyuka, kiwon lafiya, wadatar abinci da ilimi.”

Sakatare janar na majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres, ya shaida wa shugabannin cewa taron na da bukatar yin tsarin da kowa zai ji a jikinsa ya dace a aiwatar ba wai a zana a watse ba kawai.

Guterres ya ce, kasashe da dama har yanzu suna fama da radadin illar da annobar Korona ta musu da kuma na dumamar yanayi, da yakin Ukraine da dai sauransu.

Guterres ya kara da cewa, kasashen Afirka ba su samu wadataccen hanyoyin biyan basukan da suke makale a wuyayensu, da hakan ke barazanar cewa nan gaba al’ummar da ke tasowa za su iya shiga mawuyacin hali sakamakon wannan tulin basukan.

Ya ce, tsarin yarjejeniyar kudin na da bukatar ya duba wadannan matsalolin ta yadda za a shigar cikin tsarin domin shawo kan tulin matsalolin da suke akwai, ya nuna damuwarsa kan basukan da ke kan kasashen Afrika, inda ya nuna hasken cewa ta hanyar kyakkyawar tsarin da aiki tukuru za a iya magance wasu daga cikin matsalolin.

Sakataren ya nuna bukatar da ke akwai ga shugabannin duniya da su hada hannu wajen fuskantar matsalolin da suke akwai domin samar da mafita da cigaban kasashe masamman masu tasowa.

Wani masani kan dumamar yanayi, Vanessa Nakate, da ya fito daga kasar Uganda, ya yi nemi a dan yi shiru domin jinjina wa marasa galihu da wadanda suke cikin mawuyacin hali a duniya, yana mai cewa karya al’kawura idan aka dauka na gurguntar da rayuwar mutane da dama a kasashe masu tasowa.

Tunin shugabannin da jagororin manyan kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyi suka tsunduma cikin taron domin nema hanyoyin da za a fitar da tsarin yarjejeniya da ake kyautata zaton zai taimaka sosai wajen rage talauci da basuka a kasashen duniya.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Tinubu
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Tinubu

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Tinubu

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.