ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Hadu Da Shugabannin Duniya A Faransa Don Tunkarar Matsalar Talauci Da Basuka

Macron, Guterres Sun Bukaci A Samar Da Sabon Tsarin Hada-hadar Kudi Na Duniya

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis ya hadu tare da sauran shugabannin kasashen duniya a Paris-France a wajen babban taron kan yarjejeniyar kwaskwarima ga tsarin hada-hadar kudi na duniya, wacce kai tsaye hakan zai taimaka wajen rage kaifin talauci, shawo kan basuka ko sokewa da kuma la’akari da kananun kasashen da annobar Korona ta raunata.

Tinubu ya halarci wurin taron da ke Palais Brongniart, da karfe 8.59 am agogon Nijeriya domin halartar bude taron sabon tsarin hada-hadar kudi na duniya, inda ya samu tarba daga ministan Faransa da ke kula da harkokin kasashen waje, Catherine Colonna.

  • Li Qiang: Alakar Kasashen Sin Da Faransa Tana Da Ma’ana A Duniya.

A sanarwar manema labarai, Dele Alake, da yake marabtar bakin, shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron, ya ce, babban taron na da manufar hada tunani waje guda ne domin samar da sabon tsarin hada-hadar kudi na duniya wanda hakan zai taimaka sosai wa kasashe masu tasowa wajen sauyin makamashi, yaki da talauci da fatara, tare da muunta ‘yancin kowace qasa domin kyautata rayuwa.

ADVERTISEMENT

Shugaban na Faransa, ya kara cewa kasashen Afrika suna kan gaba wajen fuskantar manyan matsaloli, tare da tulin basuka da suke janyo koma baya ga cigaban kasashen, don haka ya ce, taron zai taimaka wajen fuskantar irin wadannan matsalolin domin neman mafiya.

“Annobar Korona ta janyo wahala da mawuyacin yanayi matuka, yanzu muna fuskatar yakin Ukraine da ya janyo babban matsala ga tattalin arziki,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Macron ya shaida wa shugabannin kasashen 50, akwai bukatar sake zurfin nazari wajen ganin yadda za a tafiyar da kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyi domin ganin kowani bangare na amfanuwa da juna tare da maida hankali kan masu rauni don a tafi tare.

Ya ce, babban matsalar fatara da talauci tabbas na bukatar hada karfi da karfe tare da fito da muhimman dabaru da hikomin shawo kansa, “Ya kamata dukkaninmu mu yarda cewa babu wata kasa da za ta iya magance matsalar fatara ita kadai,” ya kara.

Macron ya ce, tsarin da za a fitar din zai hada da masu ruwa da tsari a kasashen, shiyoyi, shigo da kamfanoni da cibiyoyi masu zaman kasnu musamman irin International Monetary Fund da bankin duniya World Bank domin fito da matakan kawo gyara.

Ya sake nanata cewa kamfanoni masu zaman kansu na da gayar muhimmanci a janyo su jika wajen fitar da sabon tsari domin fuskantar cigaba mai ma’ana, kazalika, ya ce, a irin lokacin da ake neman kawo sauyi ga sashin hada-hadar kudade akwai wasu fannonin da suke bukatar kula da suka hada da kiwon lafiya, ilimi da wadatar abinci.

A madadin kasashen Afrika kuwa, shugaban jamhuriyar Nijar, Mohammed Bazoum, ya ce, dole sabon yarjejeniyar ya kasance cikin hanzari da muhimmanci ga Afrika sannan, tsarin da za a fitar din a yi wajen tsage gaskiya domin tabbatar da a zahirance kasashe masu tasowa sun amfana a matsayin abokan jere.

Bazoum ya ce, matsalolin talauci da kwararowar hamada sun addabi kasashensu, da ke shafar zaman lafiya da kwanciyar hankali a nahiyar.

A cewarsa, “A Afirka muna bukatar taimako wajen shimfida ayyuka, kiwon lafiya, wadatar abinci da ilimi.”

Sakatare janar na majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres, ya shaida wa shugabannin cewa taron na da bukatar yin tsarin da kowa zai ji a jikinsa ya dace a aiwatar ba wai a zana a watse ba kawai.

Guterres ya ce, kasashe da dama har yanzu suna fama da radadin illar da annobar Korona ta musu da kuma na dumamar yanayi, da yakin Ukraine da dai sauransu.

Guterres ya kara da cewa, kasashen Afirka ba su samu wadataccen hanyoyin biyan basukan da suke makale a wuyayensu, da hakan ke barazanar cewa nan gaba al’ummar da ke tasowa za su iya shiga mawuyacin hali sakamakon wannan tulin basukan.

Ya ce, tsarin yarjejeniyar kudin na da bukatar ya duba wadannan matsalolin ta yadda za a shigar cikin tsarin domin shawo kan tulin matsalolin da suke akwai, ya nuna damuwarsa kan basukan da ke kan kasashen Afrika, inda ya nuna hasken cewa ta hanyar kyakkyawar tsarin da aiki tukuru za a iya magance wasu daga cikin matsalolin.

Sakataren ya nuna bukatar da ke akwai ga shugabannin duniya da su hada hannu wajen fuskantar matsalolin da suke akwai domin samar da mafita da cigaban kasashe masamman masu tasowa.

Wani masani kan dumamar yanayi, Vanessa Nakate, da ya fito daga kasar Uganda, ya yi nemi a dan yi shiru domin jinjina wa marasa galihu da wadanda suke cikin mawuyacin hali a duniya, yana mai cewa karya al’kawura idan aka dauka na gurguntar da rayuwar mutane da dama a kasashe masu tasowa.

Tunin shugabannin da jagororin manyan kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyi suka tsunduma cikin taron domin nema hanyoyin da za a fitar da tsarin yarjejeniya da ake kyautata zaton zai taimaka sosai wajen rage talauci da basuka a kasashen duniya.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

Wakilin Sin Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Kan Batun Da Ya Shafi Jihar Xinjiang

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.