• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Himmatu Wajen Kammala Titin Abuja Zuwa Kano Cikin Watanni 14 – Minista

by Sulaiman
9 months ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da jajircewar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake yi na kammala aikin titin Abuja zuwa Kano cikin wata 14.

 

Da yake magana yayin wata ziyara ta duba aikin a garin Tafa, Jihar Neja, a ranar Alhamis, Idris ya bayyana cewa jajircewar Shugaban Ƙasa wajen hanzarta aikin ya sa aka bai wa wani kamfani kwangilar wasu sassan aikin da aka fara bai wa kamfanin Julius Berger PLC.

  • Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah
  • An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

Ya ce: “Shugaban Ƙasa ya himmatu matuƙa wajen ganin an kammala aikin titin Abuja zuwa Kano da ta ratsa Kaduna da Zariya, kuma ya dage cewa dole a kammala wannan aiki. Ba za mu bari wani ɗan kwangila ya tilasta wa gwamnati ta bi sharuɗɗanshi kan wannan aiki ko wani aiki ba. Ba mu da isasshen lokaci na jira na tsawon wasu shekaru uku kafin a kammala wannan titi.

 

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

“Ministan Ayyuka ya bayyana cewa sun sanya wa kan su wa’adin watanni 14 don kammala wannan titi.

“Ganin irin ƙwazo da jajircewar da suke nunawa, mun yi imani za a cika wannan wa’adi.

 

“Ga waɗanda suke siyasantar da wannan aikin titi, don Allah ku ajiye siyasa a gefe. Wannan titi dole ne a kammala shi. Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya himmatu matuƙa wajen ganin wannan babbar hanyar da ke haɗa Abuja da Kano da sauran jihohi an kammala ta. Babu abin da zai hana hakan.”

 

Idris ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa ya ƙi amincewa da wa’adin shekaru uku da kamfanin Julius Berger ya bayar, inda ya ba da umarnin kammala aikin a cikin gaggawa.

 

An raba aikin zuwa kashi uku domin sauƙaƙa gudanarwa da tabbatar da cewa an kammala shi cikin lokaci.

 

Idris, wanda ya samu rakiyar Ministan Ayyuka, Sanata Dave Umahi, da wasu manyan jami’ai, ya yaba wa jajircewar Umahi, inda ya jinjina masa kan ƙoƙarin sa wajen rage kuɗin kwangilar da kuma wa’adin kammalawa.

 

Ya bayyana cewa da farko Julius Berger sun nemi ƙarin kuɗin kwangilar daga Naira biliyan 797 zuwa Naira tiriliyan 1.5 tare da ƙarin wa’adi zuwa shekaru uku.

 

Sanata Umahi ya bayyana cewa ma’aikatar ta samu amincewa daga Hukumar Kula da Sayen Kayayyaki ta Ƙasa (BPP) kan sabon kuɗin kwangilar Naira biliyan 252.89, wanda za a gabatar wa Majalisar Zartaswa ta Tarayya domin amincewa.

 

Sabon tsarin ya haɗa da ƙarin wasu kilomita a ɓangaren Kano, sanya wutar lantarki mai amfani da hasken rana, da kuma tanadi don kula da titin a nan gaba.

 

Idris ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su daina siyasantar da aikin, su mayar da hankali kan ganin an kammala shi, yana mai jaddada muhimmancin sa wajen haɗa Babban Birnin Tarayya da Kano da sauran jihohin arewa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe
Labarai

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra
Labarai

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
Next Post
Sojojin Sin Sun Gudanar Da Sintirin Hadin Gwiwa Na Shirin Ko Ta Kwana A Tekun Kudancin Kasar

Sojojin Sin Sun Gudanar Da Sintirin Hadin Gwiwa Na Shirin Ko Ta Kwana A Tekun Kudancin Kasar

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.