• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Himmatu Wajen Kammala Titin Abuja Zuwa Kano Cikin Watanni 14 – Minista

by Sulaiman
4 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Himmatu Wajen Kammala Titin Abuja Zuwa Kano Cikin Watanni 14 – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya tabbatar da jajircewar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake yi na kammala aikin titin Abuja zuwa Kano cikin wata 14.

 

Da yake magana yayin wata ziyara ta duba aikin a garin Tafa, Jihar Neja, a ranar Alhamis, Idris ya bayyana cewa jajircewar Shugaban Ƙasa wajen hanzarta aikin ya sa aka bai wa wani kamfani kwangilar wasu sassan aikin da aka fara bai wa kamfanin Julius Berger PLC.

  • Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah
  • An Gudanar Da Somin-Tabin Shirye-Shiryen Murnar Bikin Bazara Na CMG A New York

Ya ce: “Shugaban Ƙasa ya himmatu matuƙa wajen ganin an kammala aikin titin Abuja zuwa Kano da ta ratsa Kaduna da Zariya, kuma ya dage cewa dole a kammala wannan aiki. Ba za mu bari wani ɗan kwangila ya tilasta wa gwamnati ta bi sharuɗɗanshi kan wannan aiki ko wani aiki ba. Ba mu da isasshen lokaci na jira na tsawon wasu shekaru uku kafin a kammala wannan titi.

 

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

“Ministan Ayyuka ya bayyana cewa sun sanya wa kan su wa’adin watanni 14 don kammala wannan titi.

“Ganin irin ƙwazo da jajircewar da suke nunawa, mun yi imani za a cika wannan wa’adi.

 

“Ga waɗanda suke siyasantar da wannan aikin titi, don Allah ku ajiye siyasa a gefe. Wannan titi dole ne a kammala shi. Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya himmatu matuƙa wajen ganin wannan babbar hanyar da ke haɗa Abuja da Kano da sauran jihohi an kammala ta. Babu abin da zai hana hakan.”

 

Idris ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa ya ƙi amincewa da wa’adin shekaru uku da kamfanin Julius Berger ya bayar, inda ya ba da umarnin kammala aikin a cikin gaggawa.

 

An raba aikin zuwa kashi uku domin sauƙaƙa gudanarwa da tabbatar da cewa an kammala shi cikin lokaci.

 

Idris, wanda ya samu rakiyar Ministan Ayyuka, Sanata Dave Umahi, da wasu manyan jami’ai, ya yaba wa jajircewar Umahi, inda ya jinjina masa kan ƙoƙarin sa wajen rage kuɗin kwangilar da kuma wa’adin kammalawa.

 

Ya bayyana cewa da farko Julius Berger sun nemi ƙarin kuɗin kwangilar daga Naira biliyan 797 zuwa Naira tiriliyan 1.5 tare da ƙarin wa’adi zuwa shekaru uku.

 

Sanata Umahi ya bayyana cewa ma’aikatar ta samu amincewa daga Hukumar Kula da Sayen Kayayyaki ta Ƙasa (BPP) kan sabon kuɗin kwangilar Naira biliyan 252.89, wanda za a gabatar wa Majalisar Zartaswa ta Tarayya domin amincewa.

 

Sabon tsarin ya haɗa da ƙarin wasu kilomita a ɓangaren Kano, sanya wutar lantarki mai amfani da hasken rana, da kuma tanadi don kula da titin a nan gaba.

 

Idris ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su daina siyasantar da aikin, su mayar da hankali kan ganin an kammala shi, yana mai jaddada muhimmancin sa wajen haɗa Babban Birnin Tarayya da Kano da sauran jihohin arewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar Tsaro Ta Kashe ‘Yan Bindiga 7, Ta Kwato Shanu 109 Da Aka Sace A Katsina

Next Post

Sojojin Sin Sun Gudanar Da Sintirin Hadin Gwiwa Na Shirin Ko Ta Kwana A Tekun Kudancin Kasar

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

1 hour ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

3 hours ago
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

5 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

7 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

9 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

12 hours ago
Next Post
Sojojin Sin Sun Gudanar Da Sintirin Hadin Gwiwa Na Shirin Ko Ta Kwana A Tekun Kudancin Kasar

Sojojin Sin Sun Gudanar Da Sintirin Hadin Gwiwa Na Shirin Ko Ta Kwana A Tekun Kudancin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.