• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah

by Abba Ibrahim Wada
6 months ago
in Labarai
0
Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Mohamed Salah ya ce babu wata alama dake nuna tsawaita kwanginsa da kungiyar tasa, kuma da ”kamar wuya” hakan ta kasance saboda har yanzu babu wata magana mai karfi tsakaninsa da shugabannin kungiyar duk da cewa magoya baya suna ta kiraye-kirayen cewa ya kamata ya sake sabon kwantiragi a kungiyar wadda take mataki na daya a teburin gasar Premier.

Salah, dan asalin kasar Masar ya shiga wata shidan karshe na kwantiraginsa, kuma a yanzu zai iya tattaunawa da kungiyoyin da ba na Ingila ba, kan makomarsa idan kwantiraginsa ya kare a wannan kaka inda a kwanakin baya a ke ci gaba da danganta dan wasan da komawa kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German, sannan kungiyoyi daga kasar Saudiyya ma suna bibiyar halin da yake ciki a Liberpool din.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)
  • Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano

Dan wasan mai shekara 32 a duniya ya koma Liberpool ne daga Roma a shekarar 2017, kuma a wannan kaka ya zura kwallo 20 a duka wasannin da ya buga wa kungiyar a bana, lamarin da ya taimaka wa kungiyar darewa teburin Premier da na Gasar Zakarun Turai kuma a yanzu haka dan wasan ne kan gaba a yawan zura kwallo a gasar Premier, inda ya ci 17, uku fiye da Erling Haaland na Man City.

Da aka tambaye shi, ko yana tunanin wannan ce kakarsa ta karshe a Anfield? sai ya amsa da cewa ”ya zuwa yanzu dai haka ne, saura wata shida domin babu alamun ci gaba da zamansa a kungiyar, Salah, wanda a baya ya buga wasa a kungiyoyin Chelsea da Basel da Fiorantina ya kara da cewa da alama ba za su daidaita ba, amma dai suna jira su gani shi da wakilansa.

Sai dai a baya-bayan nan Salah na yawan magana da kafafen yada labarai game da makomarsa a Liberpool, sannan a watan Satumbar shekarar da ta gabata ma, lokacin da Liberpool ta doke Manchester United, dan wasan ya ce ya buga wasan ne tamkar wasansa na karshe a Old Trafford, sannan ya maimaita kalaman nasa a lokacin da suka doke Manchester City a watan da ya gabata.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Shi ma kaftin din kungiyar, Birgil ban Dijk da Trent Aledander-Arnold kwantiraginsu zai kare a karshen wannan kakar kuma ana danganta shi da komawa kasar Saudiyya da buga wasa ko kuma kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, har ila yau ana alakanta Aledander-Arnold, wanda shima kwantiranginsa zai kare a kungiyar ta Liberpool da komawa kungiyar Real Madrid.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: LiverpoolSalah
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Kwacen Waya: Fusatattun Matasa Sun Bankawa Keken Adaidaita Sahu Wuta A Kano

Next Post

Turji Na Neman Hanyar Tsira Yayin Da Sojoji Suka Farmaki Mayaƙansa Tare Da Harbe Ɗansa 

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

5 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da ÆŠansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

9 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

9 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

12 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

13 hours ago
Next Post
turji

Turji Na Neman Hanyar Tsira Yayin Da Sojoji Suka Farmaki Mayaƙansa Tare Da Harbe Ɗansa 

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A ZaÉ“en 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.