ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ba Zan Ci Gaba Da Zama A Liverpool Ba -Salah

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Salah

Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Mohamed Salah ya ce babu wata alama dake nuna tsawaita kwanginsa da kungiyar tasa, kuma da ”kamar wuya” hakan ta kasance saboda har yanzu babu wata magana mai karfi tsakaninsa da shugabannin kungiyar duk da cewa magoya baya suna ta kiraye-kirayen cewa ya kamata ya sake sabon kwantiragi a kungiyar wadda take mataki na daya a teburin gasar Premier.

Salah, dan asalin kasar Masar ya shiga wata shidan karshe na kwantiraginsa, kuma a yanzu zai iya tattaunawa da kungiyoyin da ba na Ingila ba, kan makomarsa idan kwantiraginsa ya kare a wannan kaka inda a kwanakin baya a ke ci gaba da danganta dan wasan da komawa kungiyar kwallon kafa ta Paris Saint German, sannan kungiyoyi daga kasar Saudiyya ma suna bibiyar halin da yake ciki a Liberpool din.

  • Ayyukan Jami’an Ilimi Da Muhimmancinsu (3)
  • Ƴansanda Sun Gano Motoci 2 Da Aka Sace A Kano

Dan wasan mai shekara 32 a duniya ya koma Liberpool ne daga Roma a shekarar 2017, kuma a wannan kaka ya zura kwallo 20 a duka wasannin da ya buga wa kungiyar a bana, lamarin da ya taimaka wa kungiyar darewa teburin Premier da na Gasar Zakarun Turai kuma a yanzu haka dan wasan ne kan gaba a yawan zura kwallo a gasar Premier, inda ya ci 17, uku fiye da Erling Haaland na Man City.

ADVERTISEMENT

Da aka tambaye shi, ko yana tunanin wannan ce kakarsa ta karshe a Anfield? sai ya amsa da cewa ”ya zuwa yanzu dai haka ne, saura wata shida domin babu alamun ci gaba da zamansa a kungiyar, Salah, wanda a baya ya buga wasa a kungiyoyin Chelsea da Basel da Fiorantina ya kara da cewa da alama ba za su daidaita ba, amma dai suna jira su gani shi da wakilansa.

Sai dai a baya-bayan nan Salah na yawan magana da kafafen yada labarai game da makomarsa a Liberpool, sannan a watan Satumbar shekarar da ta gabata ma, lokacin da Liberpool ta doke Manchester United, dan wasan ya ce ya buga wasan ne tamkar wasansa na karshe a Old Trafford, sannan ya maimaita kalaman nasa a lokacin da suka doke Manchester City a watan da ya gabata.

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

Shi ma kaftin din kungiyar, Birgil ban Dijk da Trent Aledander-Arnold kwantiraginsu zai kare a karshen wannan kakar kuma ana danganta shi da komawa kasar Saudiyya da buga wasa ko kuma kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid, har ila yau ana alakanta Aledander-Arnold, wanda shima kwantiranginsa zai kare a kungiyar ta Liberpool da komawa kungiyar Real Madrid.

Salah
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso

MASU ALAKA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje
Labarai

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana
Labarai

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Next Post
turji

Turji Na Neman Hanyar Tsira Yayin Da Sojoji Suka Farmaki Mayaƙansa Tare Da Harbe Ɗansa 

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.