• English
  • Business News
Sunday, May 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Naɗa Ministan Yada Labarai Cikin Kwamitin Yi Wa Shirin Tallafi Garambawul

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Tinubu ya kafa kwamitin ministoci shida wanda zai yi wa Shirin Inganta Rayuwar Marasa Galihu (NSIP) garambawul.

Kafa kwamitin ya biyo bayan dakatar da shirin da Tinubu ya yi, mako ɗaya bayan dakatar da Ministar Harkokin Agaji da Jinƙai, Dakta Betta Edu.

  • Ofishin Kula Da Harkokin Taiwan Na Majalisar Gudanarwa Da Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Sun Yi Tsokaci Kan Sakamakon Zabukan Taiwan
  • AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

Shugaban Ƙasar ya dakatar da Edu ne bayan sauke jagorar raba Tattalin Marasa Galihu, Hajiya Halima Shehu.

An zargi Edu da karkatar da naira miliyan 585.2 cikin asusun bankin wata ma’aikaciyar gwamnati.

Cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labarai na Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Asabar, ya ce kwamitin da Tinubu ya naɗa ya ƙunshi ministoci shida ƙarƙashin Ministan Harkokin Kuɗaɗe, kuma Ministan Kula da Tattalin Arziki, Mista Wale Edun.

Labarai Masu Nasaba

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

Sauran sun haɗa da Ministan Yaɗa Labarai da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris; Ministan Lafiya, Dakta Ali Pate, da Ministan Kasafi Da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Abubakar Bagudu.

Akwai kuma Ministan Sadarwa da Ƙaramin Ministan Harkokin Matasa.

Ngelele ya bayyana nauyin da aka ɗora wa kwamitin, inda ya ce: “An ɗora wa Kwamitin Musamman na Shugaban Ƙasa nauyin gaggauta fara bin diddigin kashe kuɗaɗen Shirin Inganta Rayuwar Marasa Galihu da kuma duba tsare-tsare da ƙa’idojin shirin baki ɗaya.

“Za su yi haka ne domin sake wa shirin fasalin tsare-tsaren raba kuɗaɗe a ayyukan tallafin marasa galihu, shirin ciyar da ‘yan makaranta da tallafa wa masu ƙananan sana’o’i. Sai kuma Shirin N-Power da na tallafin kuɗaɗe ga marasa galihu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Betta EduJin kaiN-PowerNSIP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Soyayyar Kananan Yara: A Ina Gizo Yake Sakar?

Next Post

Kano: Sanusi Lamido Ya Soki Gawuna Kan Rashin Karɓar Faɗuwa Zaɓe A Karon Farko

Related

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF
Labarai

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

6 hours ago
Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 
Labarai

Budurwa ƴar shekara 15 Ta Jefar Da Jariri A Sansanin Ƴan Gudun Hijira A Borno 

12 hours ago
NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal
Labarai

NNPCL Ta Rufe Matatar Mai Ta Fatakwal

12 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mazauna Kauyuka 4 A Taraba Bayan Taron Zuba Jari

13 hours ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

16 hours ago
Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari

19 hours ago
Next Post
Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi ll

Kano: Sanusi Lamido Ya Soki Gawuna Kan Rashin Karɓar Faɗuwa Zaɓe A Karon Farko

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.