ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

AFCON 2023: ‘Yan Wasan Da Za Su Haskaka A Gasar Kofin Afirka

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
AFCON

Kamar yadda aka tsara, a yau 13 ga watan Janairu aka fara gasar cin kofin Afirka karo na 34, kuma za a kammala ranar 11 ga watan Fabrairu a kasar Ibory Coast, wadda itace mai masaukin baki.

Sai dai gasar ta wannan karon za ta samu bakuncin zakakuran ‘yan wasa da tauraruwarsu take haskawa a duniya kuma sun buga wasanni a gasar a shekarun baya kuma har yanzu suna haskawa.

 

ADVERTISEMENT

Muhammad Salah (Masar)

Masar ta yi rashin nasarar lashe kofin a hannun Senegal a shekara ta 2022 a Kamaru, sannan Senegal din ta hana Masar zuwa gasar Kofin Duniya da aka yi a kasar Katar a 2022. Dukkan wasannin a bugun fenariti Senegal ta yi nasara – kuma Salah bai buga fenaritin ba a AFCON, wanda shi ne na karshen bugawa, kuma kafin nan Senegal ta lashe kofin saboda ‘yan Masar ba su ci da yawa ba.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Kofin AFCON na bakwai da Masar ta dauka shi ne a shekarar 2010, kuma Salah na fatan taka rawar gani fiye da wadda ya yi a Gabon a 2017 da kuma a Kamru a shekarar 2022.

Salah ya dauki kofuna da yawa a Liberpool, sai dai zai so ya kara cin kwallo bayan shidan da ya zura a raga daga AFCON ukun da ya halarta, sannan yana son ya jagoranci Masar ta lashe gasar.

Kamar yadda yake taka rawar gani a Liberpool, a bana, Salah ne zai ja ragamar kasar a fafatawa da Ghana da Cape Berde da Mozambikue a rukuni na biyu.

 

Victor Osimhen (Nijeriya)

Dan wasa Bictor Osimhen ne ya lashe gwarzon dan kwallon Afirka na 2023 a bikin da aka yi ranar 11 ga watan Disamba sannan ya zama na farko da ya lashe kyautar daga Nijeriya tun bayan shekara ta 1999.

A shekara 2021 bai samu zuwa gasar ba sakamakon bullar cutar korona da raunin da ya ji, sai dai shin ko wanda ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon Afirka na bana zai ja ragamar Super Eagles ta lashe kofin na 2024?

Osimhen mai shekara 24 ya zama daya daga fitattun masu cin kwallaye a Turai, wanda ya zama kan gaba a cin kwallaye a SerieA, kuma hakan ya sa Napoli ta lashe kofin a karon farko tun bayan 1990.

Jinya da Osimhen ya yi ya sa Super Eagles ta yi canjaras da Lesotho da kuma Zimbabwe a wasan shiga gasar Kofin Duniya da za a yi a 2026, sannan tsohon dan wasan Lille din yana cikin tawagar Super Eagles a AFCON 2019, amma daga baya aka saka shi a wasan da kasar ta zama ta uku a wasannin.

Nijeriya tana rukunin da ya hada da mai masaukin baki Ibory Coast da Ekuatorial Guinea da Guinea-Bissau a rukunin farko.

 

Serhou Guirassy (Guinea)

Dan wasan na taka rawar gani a kungiyar kwallon kafa ta Stuttgard ta kasar Jamus, wanda ya ci kwallo 15 a wasanni 10 a gasar Bundesliga kuma dan wasan mai shekara 27, tsohon matashin tawagar Faransa zai buga AFCON a karon farko, bayan da ya fara yi wa Guine wasa a Maris din shekara ta 2022.

Rukuni na uku za a yi wasannin hamayya da ya kunshi mai rike da kofin Senegal da Kamaru, inda Syli National ke ciki da Gambia, wadda karo na biyu kenan da za ta kara a wasannin.

Raunin da ya ji a watan Nuwamba ya kawo masa tsaiko, amma dai Guinea na fatan Guirassy zai sa kwazon da zai kai kasar zagaye na biyu, inda daga nan komai zai iya faruwa.

 

Mohammed Kudus (Ghana)

Dan wasa Mohammed Kudus ya ci kwallo biyu lokacin da Ghana ta doke South Korea a gasar Kofin Duniya ta 2022 a Katar kuma Ghana za ta ziyarci makwabciyarta Ibory Coast da fatan ba za ta maimaita abin kunya da ta yi a Kamaru ba, inda aka fitar da ita a wasannin rukuni – har da wanda Comoros ta doke ta 3-2.

Ghana tana tangal-tangal a wasa biyu da ta buga a neman shiga gasar kofin duniya da za a yi a 2026, wadda ta kara rashin nasara a hannun Comoros, sannan Kudus ne kan gaba a cin kwallaye da kasar ta samu gurbin zuwa Ibory Coast mai uku a raga, kuma yana taimaka wa West Ham United a wasan da take bugawa tun bayan da ya koma kungiyar da ke buga Premier League a cikin watan Agusta daga Ajad ta Holland.

Bayan da ya ci kwallo biyu a kofin duniya a Katar a 2022, ko dan wasan mai shekara 23 zai ja ragamar kasar ta taka rawar gani a Ibory Coast?

 

Azzedine Ounahi (Morocco)

Dan wasa Azzedine Ounahi yayi kokari sosai kuma rawar da dan wasan ya taka a gasar kofin duniya a Katar a 2022 a tawagar Morocco da ta kafa tarihin kai wa dab da karshe ta farko a Afirka – hakan ya sa Marseille ta dauki Ounahi.

Sai dai ya sha jinya tun raunin da ya ji a lokacin da yake buga wa tawagar Morocco wasa a watan Maris, bayan wasa bakwai da ya buga wa sabuwar kungiyarsa ta kasar Faransa.

Ounahi mai shekara 23 na aiki tukuru domin ya taka rawar gani a AFCON, koma ya yi fiye da kwazon da ya saka a gasar Kofin Duniya – sai dai dan wasan bai yi wa Morocco karawa biyu a neman shiga Kofin Duniya ba da ta yi a cikin Nuwamba. Kociyan tawagar, Walid Regragui zai so yin amfani da dan wasan da ya bayar da gudunmuwar da suka kai dab da karshe a kofin duniya, yayin da Morocco ke rukuni na shida da ya hada da Jamhurirae Congo da Zambia da kuma Tanzania.

Kofin afirka
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin ‘Yan Wasansa Na Yau

AFCON 2023: Hasashen Yadda Kocin Super Eagles Zai Yi Zubin 'Yan Wasansa Na Yau

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.