Shugaba Bola Tinubu ya sanya hannu kan wata sabuwar doka ta musamman da za ta rage farashin haƙo mai da iskar gas a Nijeriya. Wannan mataki na da nufin jawo sabbin masu zuba jari da kuma ƙara kuɗaɗen shiga na gwamnati.
Dokar da ake kira ‘Dokar Taimako Don Rage Farashin Ayyukan Mai Da Iskar Gas, 2025’ za ta ba da gudummawar haraji ga kamfanonin mai da gas da suka rage farashin ayyukansu bisa ƙa’idojin masana’antu. Kamfanonin da suka cimma waɗannan mataki za su iya samun kashi 50% na ƙarin kuɗin da gwamnati za ta samu daga rage farashin.
- Za Mu Ci Gaba Da Aikin Neman Man Fetur Arewacin Nijeriya — Ojulari
- Tsadar Farashin Ƙwai Ya Sa Ƴan Nijeriya Sun Haƙura Da Cinsa
Duk da haka, gudummawar harajin ba za ta wuce kashi 20% na harajin da kamfani ke biya a shekara ba, domin tabbatar da daidaito tsakanin taimakon masu zuba jari da kuma kula da kuɗin shigar gwamnati.
Shugaba Tinubu ya ce, “Wannan doka ta nuna cewa mun himmatu wajen gina masana’antar mai da gas mai inganci, da zata yi takara da juna (competition), don amfanin ’yan Nijeriya. Yana da muhimmanci ga makomar ƙasa, samar da ayyukan yi, da kuma amfani da kowace gangar mai.”
Hukumar kula da mai da Iskar Gas ta Nijeriya (NUPRC) za ta fitar da ƙa’idodin farashi na shekara-shekara don ayyuka daban-daban kamar a ƙasa, da ruwa mai zurfi, da tekun zurfi. Za a kuma fitar da cikakkun bayanai game da wannan dokar a cikin ’yan makonnin nan. Gwamnati ta yi imanin cewa wannan dokar za ta ƙara inganci a fannin mai da iskar gas.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp