• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Umarci Jakadun Nijeriya Da Su Dawo Gida

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tsadar Rayuwa: Tinubu Na Duba Yiwuwar Dawo Da Tallafin Mai Na Wucin Gadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci dukkanin jakadun Nijeriya da su dawo gida.

Ministan kula da harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, shi ne ya shaida hakan a ranar Asabar.

  • ‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP

A wata sanarwar babban hadimin ministan kan yada labarai da hulda da jama’a, Alkasim Abdulkadir, ya tabbatar da cewa dukkanin Jakadun Nijeriya an kirayesu da su dawo.

Sanarwar ta ce, “Bisa tambayar da ake ta yi dangane da wasikar kiranye ga jakadan Nijeriya a Ingila, ministan harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya warware zare da abawa da cewa dukkanin Jakadun Nijeriya ne ma aka umarta da su dawo gida bisa umarnin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bada.

“Dukkanin Jakadun Nijeriya da suke wakilci a wasu kasashe suna karkashin umarnin shugaban kasa ne, kuma shi ne ke da ikon dawo da dukkanin wani daga kowace kasa.”

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

A cewarsa, fayyace hakikanin batun ya zama musu dole ne lura da kiran da aka yi wa Jakadan Nijeriya a kasar Burtaniya, Sarafa Ishola da ya dawo.

A wasika mai dauke da kwanan wata 31 ga watan Agustan 2023 da ministan harkokin wajen ya aika wa Ishola, Tuggar na cewa, “Ina farin cikin sanar da kai matakin da shugaban kasa ya dauka na maka kiranye, hakan da ke nuni da zuwan karshen wakilcinka a matsayin babban jakadan Nijeriya a kasar Ingila.”

Kan wannan, an umarci jakadan da cewa cikin kwanaki shida ya hada bayanan barin aiki sannan ana tsammanin zai dawo Nijeriya kafin ko zuwa ranar 31 ga watan Oktoba, 2023.

“Ina amfani da wannan damar wajen nuna godiyar shugaban kasa a gareka bisa gudunmawarka da ka bayar a matsayin babban jadakan Nijeriya a Burtaniya.

“A daidai lokacin da muke tsumayar dawowarka Abuja, shugaban kasa na mika godiyarsa gareka bisa hidimta wa Nijeriya na zama babban jakadanta. Ina maka fatan samun rayuwa mai kyau a nan gaba,” wasikar ta shaida.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sana’a Ce Rufin Asirin Mace —Hindatu

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

2 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

5 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

5 hours ago
Tinubu
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

7 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

9 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

9 hours ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Tinubu

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.