• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Umarci Jakadun Nijeriya Da Su Dawo Gida

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci dukkanin jakadun Nijeriya da su dawo gida.

Ministan kula da harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Tuggar, shi ne ya shaida hakan a ranar Asabar.

  • ‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP

A wata sanarwar babban hadimin ministan kan yada labarai da hulda da jama’a, Alkasim Abdulkadir, ya tabbatar da cewa dukkanin Jakadun Nijeriya an kirayesu da su dawo.

Sanarwar ta ce, “Bisa tambayar da ake ta yi dangane da wasikar kiranye ga jakadan Nijeriya a Ingila, ministan harkokin wajen Nijeriya, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar, ya warware zare da abawa da cewa dukkanin Jakadun Nijeriya ne ma aka umarta da su dawo gida bisa umarnin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bada.

“Dukkanin Jakadun Nijeriya da suke wakilci a wasu kasashe suna karkashin umarnin shugaban kasa ne, kuma shi ne ke da ikon dawo da dukkanin wani daga kowace kasa.”

LABARAI MASU NASABA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

A cewarsa, fayyace hakikanin batun ya zama musu dole ne lura da kiran da aka yi wa Jakadan Nijeriya a kasar Burtaniya, Sarafa Ishola da ya dawo.

A wasika mai dauke da kwanan wata 31 ga watan Agustan 2023 da ministan harkokin wajen ya aika wa Ishola, Tuggar na cewa, “Ina farin cikin sanar da kai matakin da shugaban kasa ya dauka na maka kiranye, hakan da ke nuni da zuwan karshen wakilcinka a matsayin babban jakadan Nijeriya a kasar Ingila.”

Kan wannan, an umarci jakadan da cewa cikin kwanaki shida ya hada bayanan barin aiki sannan ana tsammanin zai dawo Nijeriya kafin ko zuwa ranar 31 ga watan Oktoba, 2023.

“Ina amfani da wannan damar wajen nuna godiyar shugaban kasa a gareka bisa gudunmawarka da ka bayar a matsayin babban jadakan Nijeriya a Burtaniya.

“A daidai lokacin da muke tsumayar dawowarka Abuja, shugaban kasa na mika godiyarsa gareka bisa hidimta wa Nijeriya na zama babban jakadanta. Ina maka fatan samun rayuwa mai kyau a nan gaba,” wasikar ta shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
Labarai

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Nijeriya
Labarai

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Don Fara Rigakafin Kansar Mahaifa

LABARAI MASU NASABA

peter

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa

October 10, 2025
Jonathan

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

Sin Za Ta Fara Cajin Kudi Na Musamman Ga Jiragen Ruwan Amurka

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.