• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Nijeriya Na Dandana Kudarsu A Mulkin Tinubu — PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa ‘yan Nijeriya na dandana kula luransu a karkashin jagorancin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC.

A wata sanarwa da babban sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba ya fitar a ranar Litinin da ta gabata, cewa babbar jam’iyyar adawar ta koka kan yadda Nijeriya ta shiga tsaka mai wuya a karkashin jam’iyyar APC da Tinubu yake jagoranta, wadda ba ta damu da ‘yan kasa ba, al’amarin da ya haifar da yanayi na rashin nagartaccen shugabanci a kasar nan.

  • Ba Za Mu Sake Lamuntar Kumbiya-kumbiyar Da Ake Tafkawa Wurin Fasfo Ba – Ministan Cikin Gida
  • Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Tallafawa Mali Bayan Janyewar Dakarun MINUSMA

Sanarwar ta kara da cewa, “Jam’iyyar ta firgita da yadda aka samu rashin jituwa mai tsanani tsakanin gwamnati da ‘yan kasa sakamakon rashin tsari da kuma gaggawar aiwatar da manufofin da suka kawo wahalhalu mai tsanani, rashin tsaro da kuma fargabar da tuni ke barazana ga zaman lafiyar al’umma da hadin kai da wanzuwar kasar nan.

“Rashin wayo ne da sanin ya kamata da gwamnati ta yi wajen cire tallafin man fetur da karya darajar naira wanda ya janyo tsadar rayuwa da ya gurgunta mana tattalin arzikin kasa, sannan ya durkusar da miliyoyin ‘yan kasuwa tare da jawo asarar ayyuka masu dimbin yawa da karuwar talauci da yunwa da rashin tsaro a fadin kasar nan.

“Lmarin ya janyo mummunar asarar ga masu saka hannun jari tare da ficewar kamfanonin tare da barin miliyoyin ‘yan Nijeriya neman aikin yi da gurgunta masu kanana da matsakaitan masana’antu wadanda su ne ainihin ginshikan tattalin arzikin kasarmu.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

“Abin ban tsoro ne cewa a cikin watanni biyun da suka gabata, sama da ‘yan Nijeriya miliyan 150 ba za su iya ciyar da iyalansu abinci ba, inda suke kwana da yauwa.

“Abin takaici ne yadda gwamnatin APC ke ci gaba da yaudarar ‘yan Nijeriya da bayar da tallafi na raba buhunan shinkafa 1,200 ga mutane a kowace jiha. Jam’iyyar APC ta fadada karfinta na yaudara da damfarar ‘yan Nijeriya ta hanyar shirye-shiryen marasa amfani.”

PDP ta bayyana damuwata game da abin da ta lura akwai rashin tausayi, damuwa da raba kan ‘yan kasa, idan ba a yi gaggawar magance lamarin ba zai iya harfar da mummunan rikici.”

Ta kuma bukaci ‘yan Nijeriya da su kwantar da hankalinsu su kasance masu bin doka da oda da kuma mara wa juna baya a kokarinsu na samar da kasa mai tsaro da ci gaban tattalin arziki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Jaddada Layin Da Bai Dace A Tsallaka Ba A Tattaunawar Soji Tsakanin Sin Da Amurka

Next Post

Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 day ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 day ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 day ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

Amfanin Gona Takwas Da Ake Saurin Girbewa Cikin Wata Shida

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.