• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rukunin kamfanin LEADERSHIP ta shelanta zabar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a matsayin gwarzon shekarar 2023.

A wata sanarwar da kamfanin ta fitar dauke da sanya hannun shugaba, Zainab Nda-Ishaih a ranar Litinin, ta ce LEADERSHIP, ta zabi Tinubu ne saboda yadda ya jajirce ya dage wajen tsallake tulin kalubalen da suke gabansa a ciki da wajen jam’iyyarsa ta APC har ya zama halastaccen shugaban kasar Nijeriya a zaben watan Fabrairun 2023.

  • Tinubu Ya Sake Mika Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Da Harin Bam Ya Rutsa A Tudun Biri, Kaduna 
  • Muna Fata Masu Talla A Kafafen Sada Zumunta Su Fadakar Kan Shirye-shiryen Tinubu Na Habaka Tattalin Arziki 

Sanarwar ta kuma yi nuni kan irin salon matsayar da Tinubu ya dauka duk da tulin wahalhalun da suke akwai musamman jim kadan bayan darewarsa karagar mulki na yunkurinsa na sake farfado da Nijeriya.

Bikin gabatar da lambar karramawa ta LEADERSHIP, na gudana ne a yayin babban taron mika lambar yabo da jawabai na LEADERSHIP, kuma wannan shi ne karo na 16 da jaridar ke gudanarwa. Kan hakan, ana zakulo jajirtattun ‘yan Nijeriya, hazikan ma’aikata, daidaiku, da kamfanonin da suka yi zarra a bangarori daban-daban domin karrama su.

Tsarin zabin wadanda za su amshi lambar yabon ya gudana ne a watan Nuwamba wanda manya-manyan jagororin (majalisar editoci) na jaridar da sashin kasuwanci hade da manbobin hukumar ba da shawarwari wadanda kwararru ne a bangarori daban-daban suka cimma.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

Tinubu ya kasance tsohon sanata, gwamnan farar hula har na wa’adi biyu a Jihar Legas, kuma ya amshi lambar yabon LEADERSHIP sau biyu, ya taka gagarumar rawa wajen samun nasarar APC wanda hakan ya kawo karshen mulkin PDP na shekaru 16, inda APC din ta kwace ragamar a 2015.

Duk da rawar da ya taka, ya sha gwagwarmaya a jam’iyyar na tsawon shekara takwas daga bisani ya yi kukan kura har ya samu nasarar jan ragamar komai na jam’iyyar da ma kasar nan baki daya.

A lokacin da ya shelanta aniyarsa na fitowa takara, Tinubu ya fuskanci tirjiya da koma baya daga cikin jam’iyyarsa ciki har ma da jami’an gwamnati a wancan lokacin da aka yi ta kawo abubuwan da za su iya zame masa tarnaki ga samun nasarar zama shugaban kasa ciki, wanda suka hada da rikita-rikitar canza fasalin takardun kudi da aka yi domin dakile aniyarsa na zama shugaban kasa.

Daker gwamnatin Muhammadu Buhar ta hakura ta amince ta mara masa baya har zuwa lokacin da gwamnonin APC na arewa suka tursasa gwamnatin da a mika ragamar takarar Nijeriya zuwa ga yankin kudancin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaLEADERSHIP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Mutum Ya Halaka Kansa A Jihar Adamawa

Next Post

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

7 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

9 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

9 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

11 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

13 hours ago
Next Post
Ministan Kudi

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 6, 2025
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.