• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rukunin kamfanin LEADERSHIP ta shelanta zabar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a matsayin gwarzon shekarar 2023.

A wata sanarwar da kamfanin ta fitar dauke da sanya hannun shugaba, Zainab Nda-Ishaih a ranar Litinin, ta ce LEADERSHIP, ta zabi Tinubu ne saboda yadda ya jajirce ya dage wajen tsallake tulin kalubalen da suke gabansa a ciki da wajen jam’iyyarsa ta APC har ya zama halastaccen shugaban kasar Nijeriya a zaben watan Fabrairun 2023.

  • Tinubu Ya Sake Mika Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Da Harin Bam Ya Rutsa A Tudun Biri, Kaduna 
  • Muna Fata Masu Talla A Kafafen Sada Zumunta Su Fadakar Kan Shirye-shiryen Tinubu Na Habaka Tattalin Arziki 

Sanarwar ta kuma yi nuni kan irin salon matsayar da Tinubu ya dauka duk da tulin wahalhalun da suke akwai musamman jim kadan bayan darewarsa karagar mulki na yunkurinsa na sake farfado da Nijeriya.

Bikin gabatar da lambar karramawa ta LEADERSHIP, na gudana ne a yayin babban taron mika lambar yabo da jawabai na LEADERSHIP, kuma wannan shi ne karo na 16 da jaridar ke gudanarwa. Kan hakan, ana zakulo jajirtattun ‘yan Nijeriya, hazikan ma’aikata, daidaiku, da kamfanonin da suka yi zarra a bangarori daban-daban domin karrama su.

Tsarin zabin wadanda za su amshi lambar yabon ya gudana ne a watan Nuwamba wanda manya-manyan jagororin (majalisar editoci) na jaridar da sashin kasuwanci hade da manbobin hukumar ba da shawarwari wadanda kwararru ne a bangarori daban-daban suka cimma.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

Tinubu ya kasance tsohon sanata, gwamnan farar hula har na wa’adi biyu a Jihar Legas, kuma ya amshi lambar yabon LEADERSHIP sau biyu, ya taka gagarumar rawa wajen samun nasarar APC wanda hakan ya kawo karshen mulkin PDP na shekaru 16, inda APC din ta kwace ragamar a 2015.

Duk da rawar da ya taka, ya sha gwagwarmaya a jam’iyyar na tsawon shekara takwas daga bisani ya yi kukan kura har ya samu nasarar jan ragamar komai na jam’iyyar da ma kasar nan baki daya.

A lokacin da ya shelanta aniyarsa na fitowa takara, Tinubu ya fuskanci tirjiya da koma baya daga cikin jam’iyyarsa ciki har ma da jami’an gwamnati a wancan lokacin da aka yi ta kawo abubuwan da za su iya zame masa tarnaki ga samun nasarar zama shugaban kasa ciki, wanda suka hada da rikita-rikitar canza fasalin takardun kudi da aka yi domin dakile aniyarsa na zama shugaban kasa.

Daker gwamnatin Muhammadu Buhar ta hakura ta amince ta mara masa baya har zuwa lokacin da gwamnonin APC na arewa suka tursasa gwamnatin da a mika ragamar takarar Nijeriya zuwa ga yankin kudancin kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaLEADERSHIP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Mutum Ya Halaka Kansa A Jihar Adamawa

Next Post

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

Related

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

15 minutes ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

2 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

4 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

5 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

9 hours ago
Next Post
Ministan Kudi

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.