ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Fata Masu Talla A Kafafen Sada Zumunta Su Fadakar Kan Shirye-shiryen Tinubu Na Habaka Tattalin Arziki 

by Sulaiman
2 years ago
Yajin aiki

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ƙungiyar masu saka tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai da sada zumunta su mayar da hankali wajen faɗakar da ‘yan Nijeriya kan sababbin tsare-tsaren tattalin arziki waɗanda gwamnatin Tinubu ta zo da su, waɗanda burinsu shi ne haifar da cigaban ƙasa ta fuskar tattalin arziki.

Idris ya yi kiran ne a ranar Alhamis a Abuja a lokacin buɗe babban Taron Masu Tallace-tallace na Ƙasa mai taken “Sadarwar Talla a Matsayin Mai Kawo Nagartaccen Sauyi Ga Ƙasa”.

  • Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Tinkarar Sauyin Yanayi A Duniya
  • Sojojin Somaliya Sun Kashe Mayakan Al-Shabab 60 A Yankin Tsakiyar Kasar

A cewar hadimin musamman na ministan kan yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim a wata sanarwa da ya fitar, inda yace, ministan ya samu wakilcin Darakta-Janar na Hukumar Wayar Da Kai ta Ƙasa (NOA), Mista Lanre Issa-Onilu, ya yi la’akari da muhimmiyar rawar da ƙwararrun masu sana’ar tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen yaɗa labaran da za su yi tasiri a wajen jama’a.

ADVERTISEMENT

Ya ce su na kan cikakken matsayin da za su iya jan akalar samun sauyi a tsarin tattalin arziki da zamantakewar Nijeriya ta hanyar yi wa jama’a yekuwar yadda za su ci moriyar sababbin tsare-tsaren da gwamnatin ke aiwatarwa.

Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin tallafa wa ƙananan sana’o’i, da Shirin Shugaban Ƙasa na Bada Rance Bisa Ƙa’idoji da shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa, waɗanda aka yi domin ‘yan kasuwa, masu aikatau, masu sufuri, ‘yan talla, da masu ayyukan fasaha da bada ƙananan rance.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

“Sana’o’i mafi ƙanƙanta a ƙasar nan su miliyan 1 za su ci moriyar rancen kuɗi N50,000 kowannen su, yayin da manyan sana’o’i za su ci moriyar rance daga Asusun Naira Biliyan 75 da aka tanadar.”

Ministan ya ƙara da cewa waɗannan shirye-shiryen ɗori ne a kan waɗanda da ma can an bayyana su kuma ana aiwatar da su, misali samar da motocin safa-safa masu aiki da hasken rana da gwamnatocin jihohi za su ƙaddamar, domin rage wahalar da cire tallafin man fetur ya janyo.

Ya ce duk waɗannan tsare-tsaren ba wai an yi su da ka ba ne, a’a, sai da aka tsara su a tsanake cikin Ajandar Sabuwar Fata ta Shugaban Ƙasa, wadda ta haɗa da sauya fasalin tattalin arziki don a samar da cigaba mai ɗorewa; ƙarfafa tsarin tsaro don samar da kwanciyar hankali da arziki; haɓaka aikin gona don wadata ƙasa da abinci; buɗe hanyoyin makamashi da ma’adinai don samun cigaba mai ɗorewa da kuma bunƙasa hanyoyi da gine-gine a matsayin su na turakun kawo cigaba.

Sauran su ne: bada muhimmanci ga harkokin ilimi, kiwon lafiya, da taimakon jama’a a matsayin muhimman ginshiƙan cigaban ƙasa da gaggauta faɗaɗar hanyoyin tattalin arziki ta hanyar masana’antu, aiki da komfuta, fasahohin zamani, ƙere-ƙere, da ƙirƙire-ƙirƙire.

Ministan ya ce wannan gwamnatin ta sadaukar da kan ta ne ga samar da bayanai a kan lokaci kuma ta nagartacciyar hanya, kuma ya bada tabbacin cewa zai gudanar da aikin da aka ɗora masa a buɗe kuma a mutunce.

Ya ce: “A yayin da mu ke bada bayani ba tare da ɓoye komai ba kuma a cikin nagarta, ina kira a gare ku a matsayin ku na ƙwararru da ku tattaro ƙwan ku da kwarkwatar ku ku taimaka mana domin mu isar da bayani dalla-dalla ga jama’a ba tare da wata hargowa ko sauya shi ba.”

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Sana’ar Kitso Ta Yi Min Komai – Safiya Yakubu

Sana'ar Kitso Ta Yi Min Komai - Safiya Yakubu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.