• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon mataimain shugaban kasar Nijeriya, Atiku Abubakar, ya roki jiga-jigan ‘yan adawa, Peter Obi, da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ‘yan takaran shugaban kasa a zaben 2023 na jam’iyyar LP da NNPP bi da bi domin su hada karfi da karfe wajen tabbatar da gaskiya kan tirka-tirkan takardun Tinubu.

Abubakar wanda ke magana dangane da sakamakon karatun da jami’ar Chicago ta fitar dangane da shaidar karatun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ake ta samun tirka-tirka kan lamuran.

  • Tattalin Arzikin Afirka Zai Durkushe – Bankin Duniya
  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Mutane 563 Da Muhallansu A Adamawa

“Ya ku ’yan uwana na Tarayyar Nijeriya, ya dace in yi tsokaci kan batutuwan da suka fayyace makomar zababbun gwamnati da halastaccen shugabanci a kasarmu (Nijeriya).

“Shugabancin siyasa da zama dan kasa na da matukar muhimmanci, domin su ne hanyoyin da muke hada kai don gina kasa mai aminci ga duk wanda ke zaune a cikinta. Kasarmu ta fi girman kowannenmu, kuma matsayinta a duniya yana shafar makomar duk dan cikinta – wanda ya fita ketare ko kuma yake zaune a cikinta. A matsayinmu na shugabanni, ya zama wajibi mu ci gaba da kyautata rayuwar al’ummarmu da kasa baki daya.

“Don haka ne, shugabannin da suka riga mu suka yi aiki tukuru wajen mayar da sojoji bariki da kare hakkin jama’a na yij zabe da kafa wa kanmu halastacciyar gwamnati. Zaben mu an kafa shi ne bisa doka kuma an kafa shi bisa tsarin mulki ta yadda za a samu halastacciyar gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

“Jama’a suna kallon mu a matsayinmu na shugabanni don mu mutunta wadannan dokoki kuma mu kare su. Wannan shi ne ya tara mu a nan.

“Wannan tafiyar da nake nema a gareku, ba don bukatata (Atiku Abubakar) ce kawai ba; tafiya ce ta tabbatar da halastacciyar gwamnati, tabbatar da gaskiya, adalci, da rikon amana a cikin al’amuranmu,”

“A bisa wannan, ina yin kira ga dukkan ‘yan Nijeriya masu kishi, shugabanninmu masu tunani, shugabannin addini da gargajiya, al’umma, da shugabannin siyasa.

“Musamman, Peter Obi na Jam’iyyar (LP), Rabi’u Kwankwaso na NNPP, shugabannin jam’iyyun siyasa a Nijeriya, da duk wani mai kishin kasar nan kamar ni, wanda ba ya fatan komai sai alheri ga kasar nan da ya hada hannu da mu cikin wannan aiki – yakin neman tabbatar da adalci da gaskiya a cikin kasarmu da gwamnatinmu.” Inji Atiku


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Atiku AbubakarChicago UniversityTakardun Makarantar Tinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Argentina Ta Gayyaci Messi Buga Mata Wasa Duk Da Raunin Da Ya Samu

Next Post

Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

Related

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

49 minutes ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

2 hours ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

2 hours ago
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru
Labarai

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

2 hours ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

3 hours ago
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe
Labarai

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

5 hours ago
Next Post
Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

August 23, 2025
2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.