• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
2 years ago
Atiku

Tsohon mataimain shugaban kasar Nijeriya, Atiku Abubakar, ya roki jiga-jigan ‘yan adawa, Peter Obi, da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ‘yan takaran shugaban kasa a zaben 2023 na jam’iyyar LP da NNPP bi da bi domin su hada karfi da karfe wajen tabbatar da gaskiya kan tirka-tirkan takardun Tinubu.

Abubakar wanda ke magana dangane da sakamakon karatun da jami’ar Chicago ta fitar dangane da shaidar karatun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ake ta samun tirka-tirka kan lamuran.

  • Tattalin Arzikin Afirka Zai Durkushe – Bankin Duniya
  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Mutane 563 Da Muhallansu A Adamawa

“Ya ku ’yan uwana na Tarayyar Nijeriya, ya dace in yi tsokaci kan batutuwan da suka fayyace makomar zababbun gwamnati da halastaccen shugabanci a kasarmu (Nijeriya).

“Shugabancin siyasa da zama dan kasa na da matukar muhimmanci, domin su ne hanyoyin da muke hada kai don gina kasa mai aminci ga duk wanda ke zaune a cikinta. Kasarmu ta fi girman kowannenmu, kuma matsayinta a duniya yana shafar makomar duk dan cikinta – wanda ya fita ketare ko kuma yake zaune a cikinta. A matsayinmu na shugabanni, ya zama wajibi mu ci gaba da kyautata rayuwar al’ummarmu da kasa baki daya.

“Don haka ne, shugabannin da suka riga mu suka yi aiki tukuru wajen mayar da sojoji bariki da kare hakkin jama’a na yij zabe da kafa wa kanmu halastacciyar gwamnati. Zaben mu an kafa shi ne bisa doka kuma an kafa shi bisa tsarin mulki ta yadda za a samu halastacciyar gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

“Jama’a suna kallon mu a matsayinmu na shugabanni don mu mutunta wadannan dokoki kuma mu kare su. Wannan shi ne ya tara mu a nan.

“Wannan tafiyar da nake nema a gareku, ba don bukatata (Atiku Abubakar) ce kawai ba; tafiya ce ta tabbatar da halastacciyar gwamnati, tabbatar da gaskiya, adalci, da rikon amana a cikin al’amuranmu,”

“A bisa wannan, ina yin kira ga dukkan ‘yan Nijeriya masu kishi, shugabanninmu masu tunani, shugabannin addini da gargajiya, al’umma, da shugabannin siyasa.

“Musamman, Peter Obi na Jam’iyyar (LP), Rabi’u Kwankwaso na NNPP, shugabannin jam’iyyun siyasa a Nijeriya, da duk wani mai kishin kasar nan kamar ni, wanda ba ya fatan komai sai alheri ga kasar nan da ya hada hannu da mu cikin wannan aiki – yakin neman tabbatar da adalci da gaskiya a cikin kasarmu da gwamnatinmu.” Inji Atiku

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
Labarai

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai
Labarai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Next Post
Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara

October 30, 2025
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 

October 30, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara 

October 30, 2025
Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC

October 30, 2025
Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray

October 30, 2025
Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya

October 30, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

October 30, 2025
Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

Bunkasar Fannin Kirkire-Kirkiren Fasahohi Na Sin Alheri Ne Ga Dukkanin Duniya Ba Barazana Ba

October 30, 2025
Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.