ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
3 years ago
Atiku

Tsohon mataimain shugaban kasar Nijeriya, Atiku Abubakar, ya roki jiga-jigan ‘yan adawa, Peter Obi, da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ‘yan takaran shugaban kasa a zaben 2023 na jam’iyyar LP da NNPP bi da bi domin su hada karfi da karfe wajen tabbatar da gaskiya kan tirka-tirkan takardun Tinubu.

Abubakar wanda ke magana dangane da sakamakon karatun da jami’ar Chicago ta fitar dangane da shaidar karatun shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ake ta samun tirka-tirka kan lamuran.

  • Tattalin Arzikin Afirka Zai Durkushe – Bankin Duniya
  • Ambaliyar Ruwa Ta Raba Mutane 563 Da Muhallansu A Adamawa

“Ya ku ’yan uwana na Tarayyar Nijeriya, ya dace in yi tsokaci kan batutuwan da suka fayyace makomar zababbun gwamnati da halastaccen shugabanci a kasarmu (Nijeriya).

ADVERTISEMENT

“Shugabancin siyasa da zama dan kasa na da matukar muhimmanci, domin su ne hanyoyin da muke hada kai don gina kasa mai aminci ga duk wanda ke zaune a cikinta. Kasarmu ta fi girman kowannenmu, kuma matsayinta a duniya yana shafar makomar duk dan cikinta – wanda ya fita ketare ko kuma yake zaune a cikinta. A matsayinmu na shugabanni, ya zama wajibi mu ci gaba da kyautata rayuwar al’ummarmu da kasa baki daya.

“Don haka ne, shugabannin da suka riga mu suka yi aiki tukuru wajen mayar da sojoji bariki da kare hakkin jama’a na yij zabe da kafa wa kanmu halastacciyar gwamnati. Zaben mu an kafa shi ne bisa doka kuma an kafa shi bisa tsarin mulki ta yadda za a samu halastacciyar gwamnati.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Jama’a suna kallon mu a matsayinmu na shugabanni don mu mutunta wadannan dokoki kuma mu kare su. Wannan shi ne ya tara mu a nan.

“Wannan tafiyar da nake nema a gareku, ba don bukatata (Atiku Abubakar) ce kawai ba; tafiya ce ta tabbatar da halastacciyar gwamnati, tabbatar da gaskiya, adalci, da rikon amana a cikin al’amuranmu,”

“A bisa wannan, ina yin kira ga dukkan ‘yan Nijeriya masu kishi, shugabanninmu masu tunani, shugabannin addini da gargajiya, al’umma, da shugabannin siyasa.

“Musamman, Peter Obi na Jam’iyyar (LP), Rabi’u Kwankwaso na NNPP, shugabannin jam’iyyun siyasa a Nijeriya, da duk wani mai kishin kasar nan kamar ni, wanda ba ya fatan komai sai alheri ga kasar nan da ya hada hannu da mu cikin wannan aiki – yakin neman tabbatar da adalci da gaskiya a cikin kasarmu da gwamnatinmu.” Inji Atiku

Atiku
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Atiku
Khalid Idris Doya
+ posts Bio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

Sin Da Wasu Kasashe 80 Sun Yi Kira Da A Kyautata Tsare-tsaren Tallafawa Tsoffi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.