• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Magoya Bayansa Sun Yi Amfani Da Kalaman Batanci

by Rabi'u Ali Indabawa
6 months ago
in Kasashen Ketare
0
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan takarar biyu sun zafafa yakin neman zabensu yayin da ya rage ‘yan kwanaki a garzaya rumfunan zaben a ranar Talata don zabar wanda zai gaji Shugaba Joe Biden.

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyar Republican Donald Trump ya jagoranci wani taron gangami a Dandalin Madison Skuare da ke birnin New York, inda ya fara da jero maganganun masu nasaba da kalaman nuna wariyar launin fata.

  • Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-18 Sun Mika Ragamar Aiki Ga Takwarorin Su Na Shenzhou-19

Abokan huldar tsohon shugaban kasar ma su ma sun yi ta furta irin wadannan kalamai kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

Trump wanda shahararre ne kuma fitacce a New York a gomman shekaru, yana fatan yin amfani da bikin wanda za’a yi a shahararren wurin nan da aka sani na gudanar da mashahuran wasannin kwallon raga da bukukuwan Billy Joel, domin yin sallama da amayar da cikin shi a fafatawar da zai yi da ‘yar takarar Democrat Kamala Harris, a zaben shugaban kasar, duk da dai rabon da jihar ta marawa wani dan takarar shugaban kasa na Republican baya tun a shekarar 1984.

Wasu daga cikin wadanda suka rika gabatar da jawaban bude taro sun rika yin amfani da kalmomin nuna wariyar launin fata, da kalaman da ba su dace ba wajen zaburar da dandazon wadanda suke hallara a wurin sa’oi kafin Trump ya yi Magana.

Labarai Masu Nasaba

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

Rudy Giuliani, wani wanda ya taba zama magajin garin birnin New York kuma tsohon lauyan Trump, ya yi wa Harris sharrin cewa wai tana bangaren ‘yan ta’adda a fadan da ake yi tsakanin Isra’ila da Palasdinu, yana mai cewa wai tana son kawo Falasdinawa cikin Amurka.

A wani sakon email yakin neman zaben Harris ya ce, taron gangamin Dandalin na Madison Skuare, manuniya ce ga irin hadari da rarrabuwar kawuna da ke kunshe a sakon da Trump din ke aikawa.

A gefe guda, yayin nata yakin neman zaben a ranar Lahadi, Harris ta nemi karfafa wa masu jefa kuri’a a Philadelphia, kwarin gwiwa a yankin wanda jam’iyyar Democrat ke da goyon baya sosai.

Ta nuna muhimmancin fitar masu jefa kuri’a wajen zabe don a rinjayi Trump a yankunan na karkara a Pennsylbania da yake da goyon baya.

A ranar, ta halarci ibada a coci, sannan ta ziyarci wurin aski, shagon sayar da littattafai, gidan cin abinci na kasar Puerto Rico da kuma wurin koyar da kwallon kwando ga matasa.

A lokacin wani taro a karshen rana, Harris ta ce “ba wanda zai zauna a gefe” a wannan zabe.

Ta kuma ce Trump yana mai da hankali ne kawai kan kansa yayin da ita kuma take neman shugabancin kasa domin taimakawa Amurkawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkatakaraTrump
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakarun Iran Sun Kashe ‘Yan Ta’adda A Yankin Kudu Maso Gabashin Kasar

Next Post

An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

Related

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Amurka Da Saudiyya Sun Ƙulla Yarjejeniyar Dala Biliyan 600 Kan Tsaro, Makamashi Da Fasaha

1 day ago
China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci
Kasashen Ketare

China Da Amurka Sun Yarda Da Rage Harajin Kayayyakinsu Domin Sasanta Rikicin Kasuwanci

2 days ago
Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah

1 week ago
Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa
Kasashen Ketare

Nijar Ta Soke Yarjejeniyar Tattara Bayanai Da Rasha Da Turkiyya, Ta Fara Neman Sabbin Abokan Hulɗa

1 week ago
Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini
Kasashen Ketare

Saudiyya Ta Tanadi Hukunci Mai Tsanani Ga Masu Yin Aikin Hajji Babu Takardun Izini

1 week ago
Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon
Kasashen Ketare

Mataimakin Shugaban Ƙasa Zai Wakilci Nijeriya A Rantsar Da Shugaban Gabon

2 weeks ago
Next Post
An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.