• English
  • Business News
Thursday, August 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Magoya Bayansa Sun Yi Amfani Da Kalaman Batanci

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
in Kasashen Ketare
0
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan takarar biyu sun zafafa yakin neman zabensu yayin da ya rage ‘yan kwanaki a garzaya rumfunan zaben a ranar Talata don zabar wanda zai gaji Shugaba Joe Biden.

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyar Republican Donald Trump ya jagoranci wani taron gangami a Dandalin Madison Skuare da ke birnin New York, inda ya fara da jero maganganun masu nasaba da kalaman nuna wariyar launin fata.

  • Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-18 Sun Mika Ragamar Aiki Ga Takwarorin Su Na Shenzhou-19

Abokan huldar tsohon shugaban kasar ma su ma sun yi ta furta irin wadannan kalamai kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

Trump wanda shahararre ne kuma fitacce a New York a gomman shekaru, yana fatan yin amfani da bikin wanda za’a yi a shahararren wurin nan da aka sani na gudanar da mashahuran wasannin kwallon raga da bukukuwan Billy Joel, domin yin sallama da amayar da cikin shi a fafatawar da zai yi da ‘yar takarar Democrat Kamala Harris, a zaben shugaban kasar, duk da dai rabon da jihar ta marawa wani dan takarar shugaban kasa na Republican baya tun a shekarar 1984.

Wasu daga cikin wadanda suka rika gabatar da jawaban bude taro sun rika yin amfani da kalmomin nuna wariyar launin fata, da kalaman da ba su dace ba wajen zaburar da dandazon wadanda suke hallara a wurin sa’oi kafin Trump ya yi Magana.

Labarai Masu Nasaba

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

Rudy Giuliani, wani wanda ya taba zama magajin garin birnin New York kuma tsohon lauyan Trump, ya yi wa Harris sharrin cewa wai tana bangaren ‘yan ta’adda a fadan da ake yi tsakanin Isra’ila da Palasdinu, yana mai cewa wai tana son kawo Falasdinawa cikin Amurka.

A wani sakon email yakin neman zaben Harris ya ce, taron gangamin Dandalin na Madison Skuare, manuniya ce ga irin hadari da rarrabuwar kawuna da ke kunshe a sakon da Trump din ke aikawa.

A gefe guda, yayin nata yakin neman zaben a ranar Lahadi, Harris ta nemi karfafa wa masu jefa kuri’a a Philadelphia, kwarin gwiwa a yankin wanda jam’iyyar Democrat ke da goyon baya sosai.

Ta nuna muhimmancin fitar masu jefa kuri’a wajen zabe don a rinjayi Trump a yankunan na karkara a Pennsylbania da yake da goyon baya.

A ranar, ta halarci ibada a coci, sannan ta ziyarci wurin aski, shagon sayar da littattafai, gidan cin abinci na kasar Puerto Rico da kuma wurin koyar da kwallon kwando ga matasa.

A lokacin wani taro a karshen rana, Harris ta ce “ba wanda zai zauna a gefe” a wannan zabe.

Ta kuma ce Trump yana mai da hankali ne kawai kan kansa yayin da ita kuma take neman shugabancin kasa domin taimakawa Amurkawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkatakaraTrump
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dakarun Iran Sun Kashe ‘Yan Ta’adda A Yankin Kudu Maso Gabashin Kasar

Next Post

An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

Related

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Kasashen Ketare

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

1 day ago
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
Kasashen Ketare

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

1 week ago
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

2 weeks ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

3 weeks ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

3 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

3 weeks ago
Next Post
An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

LABARAI MASU NASABA

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

Nijeriya Ta Kori Ƙarin ‘Yan Ƙasashen Waje 51 Da Aka Ɗaure Bisa Laifin Ta’addanci Da Zamba A Intanet

August 21, 2025
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

August 21, 2025
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

August 21, 2025
Boniface

Ac Milan Na Tattaunawa Da Bayern Leverkusen Akan Yunkurin Daukar Boniface

August 20, 2025
Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

Xi Jinping Zai Duba Faretin Sojoji Ta Kan Titin Chang’an A Ranar Uku Ga Watan Satumba Dake Tafe

August 20, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Cibiyoyin Bayar Da Lamuni Kan Tabbatar Da Gaskiya Da Adalci

August 20, 2025
Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

Faretin Sojoji Da Sin Za Ta Gudanar Zai Shaida Muhimmancin Zaman Lafiya Da Goyon Bayan Gaskiya Da Adalci Tsakanin Kasa Da Kasa

August 20, 2025
Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

Kasar Sin Za Ta Gabatar Da Sabbin Makamai Yayin Faretin Soja Na Ranar 3 Ga Watan Satumba

August 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.