ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Magoya Bayansa Sun Yi Amfani Da Kalaman Batanci

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

‘Yan takarar biyu sun zafafa yakin neman zabensu yayin da ya rage ‘yan kwanaki a garzaya rumfunan zaben a ranar Talata don zabar wanda zai gaji Shugaba Joe Biden.

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyar Republican Donald Trump ya jagoranci wani taron gangami a Dandalin Madison Skuare da ke birnin New York, inda ya fara da jero maganganun masu nasaba da kalaman nuna wariyar launin fata.

  • Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-18 Sun Mika Ragamar Aiki Ga Takwarorin Su Na Shenzhou-19

Abokan huldar tsohon shugaban kasar ma su ma sun yi ta furta irin wadannan kalamai kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

ADVERTISEMENT

Trump wanda shahararre ne kuma fitacce a New York a gomman shekaru, yana fatan yin amfani da bikin wanda za’a yi a shahararren wurin nan da aka sani na gudanar da mashahuran wasannin kwallon raga da bukukuwan Billy Joel, domin yin sallama da amayar da cikin shi a fafatawar da zai yi da ‘yar takarar Democrat Kamala Harris, a zaben shugaban kasar, duk da dai rabon da jihar ta marawa wani dan takarar shugaban kasa na Republican baya tun a shekarar 1984.

Wasu daga cikin wadanda suka rika gabatar da jawaban bude taro sun rika yin amfani da kalmomin nuna wariyar launin fata, da kalaman da ba su dace ba wajen zaburar da dandazon wadanda suke hallara a wurin sa’oi kafin Trump ya yi Magana.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Rudy Giuliani, wani wanda ya taba zama magajin garin birnin New York kuma tsohon lauyan Trump, ya yi wa Harris sharrin cewa wai tana bangaren ‘yan ta’adda a fadan da ake yi tsakanin Isra’ila da Palasdinu, yana mai cewa wai tana son kawo Falasdinawa cikin Amurka.

A wani sakon email yakin neman zaben Harris ya ce, taron gangamin Dandalin na Madison Skuare, manuniya ce ga irin hadari da rarrabuwar kawuna da ke kunshe a sakon da Trump din ke aikawa.

A gefe guda, yayin nata yakin neman zaben a ranar Lahadi, Harris ta nemi karfafa wa masu jefa kuri’a a Philadelphia, kwarin gwiwa a yankin wanda jam’iyyar Democrat ke da goyon baya sosai.

Ta nuna muhimmancin fitar masu jefa kuri’a wajen zabe don a rinjayi Trump a yankunan na karkara a Pennsylbania da yake da goyon baya.

A ranar, ta halarci ibada a coci, sannan ta ziyarci wurin aski, shagon sayar da littattafai, gidan cin abinci na kasar Puerto Rico da kuma wurin koyar da kwallon kwando ga matasa.

A lokacin wani taro a karshen rana, Harris ta ce “ba wanda zai zauna a gefe” a wannan zabe.

Ta kuma ce Trump yana mai da hankali ne kawai kan kansa yayin da ita kuma take neman shugabancin kasa domin taimakawa Amurkawa.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kasashen Ketare

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
Manyan Labarai

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
Kasashen Ketare

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Next Post
An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.