ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Magoya Bayansa Sun Yi Amfani Da Kalaman Batanci

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

TULSA, OK - MARCH 18: Former United States President Donald Trump stands on the floor during the Division I Mens Wrestling Championship held at the BOK Center on March 18, 2023 in Tulsa, Oklahoma. (Photo by Shane Bevel/NCAA Photos via Getty Images)

‘Yan takarar biyu sun zafafa yakin neman zabensu yayin da ya rage ‘yan kwanaki a garzaya rumfunan zaben a ranar Talata don zabar wanda zai gaji Shugaba Joe Biden.

A ranar Lahadi ne dan takarar shugaban kasa karkashin jam’iyar Republican Donald Trump ya jagoranci wani taron gangami a Dandalin Madison Skuare da ke birnin New York, inda ya fara da jero maganganun masu nasaba da kalaman nuna wariyar launin fata.

  • Rungumar Harkar Noma Mafita Ce Ga Ma’aikata Masu Ritaya
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-18 Sun Mika Ragamar Aiki Ga Takwarorin Su Na Shenzhou-19

Abokan huldar tsohon shugaban kasar ma su ma sun yi ta furta irin wadannan kalamai kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

ADVERTISEMENT

Trump wanda shahararre ne kuma fitacce a New York a gomman shekaru, yana fatan yin amfani da bikin wanda za’a yi a shahararren wurin nan da aka sani na gudanar da mashahuran wasannin kwallon raga da bukukuwan Billy Joel, domin yin sallama da amayar da cikin shi a fafatawar da zai yi da ‘yar takarar Democrat Kamala Harris, a zaben shugaban kasar, duk da dai rabon da jihar ta marawa wani dan takarar shugaban kasa na Republican baya tun a shekarar 1984.

Wasu daga cikin wadanda suka rika gabatar da jawaban bude taro sun rika yin amfani da kalmomin nuna wariyar launin fata, da kalaman da ba su dace ba wajen zaburar da dandazon wadanda suke hallara a wurin sa’oi kafin Trump ya yi Magana.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Rudy Giuliani, wani wanda ya taba zama magajin garin birnin New York kuma tsohon lauyan Trump, ya yi wa Harris sharrin cewa wai tana bangaren ‘yan ta’adda a fadan da ake yi tsakanin Isra’ila da Palasdinu, yana mai cewa wai tana son kawo Falasdinawa cikin Amurka.

A wani sakon email yakin neman zaben Harris ya ce, taron gangamin Dandalin na Madison Skuare, manuniya ce ga irin hadari da rarrabuwar kawuna da ke kunshe a sakon da Trump din ke aikawa.

A gefe guda, yayin nata yakin neman zaben a ranar Lahadi, Harris ta nemi karfafa wa masu jefa kuri’a a Philadelphia, kwarin gwiwa a yankin wanda jam’iyyar Democrat ke da goyon baya sosai.

Ta nuna muhimmancin fitar masu jefa kuri’a wajen zabe don a rinjayi Trump a yankunan na karkara a Pennsylbania da yake da goyon baya.

A ranar, ta halarci ibada a coci, sannan ta ziyarci wurin aski, shagon sayar da littattafai, gidan cin abinci na kasar Puerto Rico da kuma wurin koyar da kwallon kwando ga matasa.

A lokacin wani taro a karshen rana, Harris ta ce “ba wanda zai zauna a gefe” a wannan zabe.

Ta kuma ce Trump yana mai da hankali ne kawai kan kansa yayin da ita kuma take neman shugabancin kasa domin taimakawa Amurkawa.

Trump
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

An Zargi ‘Yar Siyasa Da Yunkurin Kashe Shugaban Kasar Malawi

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.