• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Zai Sanya Harajin Kashi 25 Kan Kayayyakin Canada Da Mexico

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
in Kasashen Ketare
0
Trump Zai Sanya Harajin Kashi 25 Kan Kayayyakin Canada Da Mexico
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zababban shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya ce zai sa harajin kashi ashirin da biyar kan dukkan kayan da aka shigar Amurka daga Mexico da Canada a ranar farko ta shugabancinsa.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, zababben shugaban kasar ya ce zai kakaba harajin har zuwa lokacin da Mexico da Canada za su dakatar da shigar da kwayoyi da kuma kwararar baki kasar ta kan iyakokinsu.

  • Tinubu Ya Taya Trump Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Amurka
  • Trump Ya Gayyaci Mark Zuckerberg Cin Abinci

Mista Trump ya kuma yi alkawarin kara kashi goma kan harajin kayan Chana har ita ma sai ta dakatar da fataucin kwayoyin zuwa Amurka.

Wakilin BBC ya ce a lokacin yakin neman zabensa, Trump ya yi barazanar sanya harajin kashi dari na kayan da ake shigarwa Amurka daga Mexico da Chana madamar ba su yi abun da ya dace ba.

A nata martanin, Chana ta ce tana daukar matakin dakile fataucin miyagun kwayoyi tun bayan yarjejeniyar da aka cimmawa tsakanin Shugaba Biden da takwaransa na Chanar, Di Jinping.

Labarai Masu Nasaba

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

Haka zalika, Donald Trump ya sha alwashin yin amfani da sojojin kasar wajen tasa keyar miliyoyin bakin hauren dake zaune a kasar ba tare da cikakkun takardu ba, shirin da ya sabawa al’adar Amurka ta yin amfani da sojoji a cikin gida.

Sai dai masana shari’a na ganin zai yi wuya a iya kalubalantarta a kotu.

Mashawartan Trump sun ce suna da niyar yin amfani da sojoji wajen gina wuraren tsare bakin hauren da basu da takardun zama ko kuma yin safararsu zuwa wajen Amurka, abin da zai bai wa jami’an tsaron kan iyaka da na kula da shige da fice kariya daga tuhuma ko tsarewa.

Masana na cewa gwamnati na da kariyar doka idan ta takaita rawar da sojojin za su taka zuwa na tallafawa, musamman a kan iyakar Amurka da Mexico, ba tare da sun yi mu’amala da wadanda ake tuhuma ba.

“Ina ganin hakan ba zai fuskanci kalubalen da zai yi nasara ba,” a cewar Ryan Burke, farfesa akan al’amuran da suka shafi aikin soja da dabarun yaki a kwalejin sojin saman Amurka, a jawabinsa na kashin kansa.

“Akwai boyayyun abubuwa da dama a cikin wadannan dokoki da basu fito karara sun ce, kai ba zaka iya aikata haka ba kai tsaye.”

Dokar tabbatar da tsaron al’umma ta 1878 (Posse Comitatus) ta haramta yin amfani da sojojin tarayya wajen aiwatar da doka a cikin kasa.

Majalisa ta yi togaciyar da ta sahalewa shugabannin kasa yin amfani da sojoji wajen tallafawa al’amura irin su yaki da haramtaccen fataucin miyagun kwayoyi da kuma lokutan tarzoma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Trump
ShareTweetSendShare
Previous Post

Arsenal Da West Ham Sun Kafa Tarihi A Wasan Da Suka Tashi 5-2 A London

Next Post

Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Kasashen Ketare

Makaman Rasha Masu Gudun Walkiya Da Ke Yi Wa Ƙasashen Turai Barazana

5 days ago
Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan
Kasashen Ketare

Girgizar Ƙasa Ta Kashe Sama da Mutune 600 A Afghanistan

2 weeks ago
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi
Kasashen Ketare

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

2 weeks ago
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida
Kasashen Ketare

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

3 weeks ago
Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha
Kasashen Ketare

Tinubu Ya Isa Brazil, Zai Nemi Masu Zuba Jarin Biliyoyi A Noma, Makamashi Da Fasaha

3 weeks ago
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda
Kasashen Ketare

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

3 weeks ago
Next Post
Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.