• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Zai Sanya Harajin Kashi 25 Kan Kayayyakin Canada Da Mexico

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
in Kasashen Ketare
0
Trump Zai Sanya Harajin Kashi 25 Kan Kayayyakin Canada Da Mexico
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zababban shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya ce zai sa harajin kashi ashirin da biyar kan dukkan kayan da aka shigar Amurka daga Mexico da Canada a ranar farko ta shugabancinsa.

A cikin wani sako da ya wallafa a shafukan sada zumunta, zababben shugaban kasar ya ce zai kakaba harajin har zuwa lokacin da Mexico da Canada za su dakatar da shigar da kwayoyi da kuma kwararar baki kasar ta kan iyakokinsu.

  • Tinubu Ya Taya Trump Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Amurka
  • Trump Ya Gayyaci Mark Zuckerberg Cin Abinci

Mista Trump ya kuma yi alkawarin kara kashi goma kan harajin kayan Chana har ita ma sai ta dakatar da fataucin kwayoyin zuwa Amurka.

Wakilin BBC ya ce a lokacin yakin neman zabensa, Trump ya yi barazanar sanya harajin kashi dari na kayan da ake shigarwa Amurka daga Mexico da Chana madamar ba su yi abun da ya dace ba.

A nata martanin, Chana ta ce tana daukar matakin dakile fataucin miyagun kwayoyi tun bayan yarjejeniyar da aka cimmawa tsakanin Shugaba Biden da takwaransa na Chanar, Di Jinping.

Labarai Masu Nasaba

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

Haka zalika, Donald Trump ya sha alwashin yin amfani da sojojin kasar wajen tasa keyar miliyoyin bakin hauren dake zaune a kasar ba tare da cikakkun takardu ba, shirin da ya sabawa al’adar Amurka ta yin amfani da sojoji a cikin gida.

Sai dai masana shari’a na ganin zai yi wuya a iya kalubalantarta a kotu.

Mashawartan Trump sun ce suna da niyar yin amfani da sojoji wajen gina wuraren tsare bakin hauren da basu da takardun zama ko kuma yin safararsu zuwa wajen Amurka, abin da zai bai wa jami’an tsaron kan iyaka da na kula da shige da fice kariya daga tuhuma ko tsarewa.

Masana na cewa gwamnati na da kariyar doka idan ta takaita rawar da sojojin za su taka zuwa na tallafawa, musamman a kan iyakar Amurka da Mexico, ba tare da sun yi mu’amala da wadanda ake tuhuma ba.

“Ina ganin hakan ba zai fuskanci kalubalen da zai yi nasara ba,” a cewar Ryan Burke, farfesa akan al’amuran da suka shafi aikin soja da dabarun yaki a kwalejin sojin saman Amurka, a jawabinsa na kashin kansa.

“Akwai boyayyun abubuwa da dama a cikin wadannan dokoki da basu fito karara sun ce, kai ba zaka iya aikata haka ba kai tsaye.”

Dokar tabbatar da tsaron al’umma ta 1878 (Posse Comitatus) ta haramta yin amfani da sojojin tarayya wajen aiwatar da doka a cikin kasa.

Majalisa ta yi togaciyar da ta sahalewa shugabannin kasa yin amfani da sojoji wajen tallafawa al’amura irin su yaki da haramtaccen fataucin miyagun kwayoyi da kuma lokutan tarzoma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Trump
ShareTweetSendShare
Previous Post

Arsenal Da West Ham Sun Kafa Tarihi A Wasan Da Suka Tashi 5-2 A London

Next Post

Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

Related

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

2 days ago
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?
Kasashen Ketare

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

4 days ago
Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje
Kasashen Ketare

Iran Ta Bayyana Sharaɗin Sasantawa Da Isra’ila – Ministan Harkokin Waje

5 days ago
Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka
Kasashen Ketare

Ba Za Mu Yarda A Yi Mana Ƙarfa-ƙarfa Ba – Ayatollah Ya Gargaɗi Amurka

1 week ago
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran
Kasashen Ketare

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

1 week ago
Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9
Kasashen Ketare

Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9

2 weeks ago
Next Post
Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

Jerin ‘Yan Wasa Uku Da Suka Zura Kwallaye 100 A Gasar Zakarun Turai

LABARAI MASU NASABA

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga

June 26, 2025
Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.