• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Atiku Ya Yi Allah Wadai Da Harbin Masu Zanga-zanga 

Ya Nemi Majalisar Dinkin Duniya Ta Sanya Ido Kan Mahukunta A Nijeriya 

by Sulaiman
1 year ago
Tinubu Da Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin Inuwar Jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya yi Allah wadai da amfani da harsashi kan ‘yan kasar da ke zanga-zangar lumana kan matsin rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki.

 

Atiku ya yi wannan kakkausar lafazi ne yayin da ake ci gaba da gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa a Nijeriya inda wasu jihohi aka samu hargitsi tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar kamar Kano da Abuja.

  • Yanzu Ne Lokacin Da Ya Dace Arsenal Ta Lashe Kofin Firimiya – Kroenke
  • Gwamnatin Kano Ta Sassauta Dokar Hana Fita

Zanga-zangar wacce aka shirya gudanarwa daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta, an samu rahotannin asarar rayuka, lalatawa tare da wawure dukiyar gwamnati da al’ummar kasa a wasu jihohin kasar.

Atiku ya bayyana matakin jami’an tsaro na yin amfani da harsashi akan masu zanga-zangar da cewa, “abu ne mai muni da ya yi kama da zamanin mulkin kama-karya na soji.”

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

 

Ya kara da cewa, “Yana da matukar muhimmanci a tunatar da gwamnati da hukumomin tsaro babban hakkin da ya rataya akansu na tabbatar da tsaro ta yadda ‘yan kasa za su iya amfani da ‘yancinsu na yin zanga-zanga ba tare da tsoro ba.

 

“Duk lokacin da jami’an tsaro suka bude wuta kan masu zanga-zangar lumana, babu abinda zai biyo baya face kara ta’azzarar hargitsi.

 

“Ina kira ga kasashen duniya da suka hada da Majalisar Dinkin Duniya da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa da su sanya ido sosai kan al’amuran da ke faruwa a Nijeriya.

 

“Ina sake jaddada shawarara ga masu zanga-zangar da su dage da yin amfani da ‘yancinsu na yin zanga-zangar lumana tare da yin watsi da duk wani nau’i na tashin hankali.

 

“Amma ya zama dole a gurfanar da masu wawure dukiyar jama’a da barnata kadarorin gwamnati a gaban kotu kamar yadda doka ta tanada, don irin waɗannan ayyukan, suna lalata halaccin zanga-zangar.

 

“Dole ne Shugaba Tinubu ya nuna jagoranci na gaskiya ta hanyar yin gaggawa da aiwatar da bukatun al’ummar Nijeriya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
Manyan Labarai

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano
Manyan Labarai

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Gwamnati Ta Bai Wa Gwamnoni Fiye Da Naira Biliyan 570 Don Tallafa Wa Talakawa - Tinubu 

LABARAI MASU NASABA

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.