• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Atiku Ya Yi Allah Wadai Da Harbin Masu Zanga-zanga 

Ya Nemi Majalisar Dinkin Duniya Ta Sanya Ido Kan Mahukunta A Nijeriya 

by Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Da Atiku
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon mataimakin shugaban kasa, kuma dan takarar shugaban kasa a karkashin Inuwar Jam’iyyar PDP a zaben da ya gabata, ya yi Allah wadai da amfani da harsashi kan ‘yan kasar da ke zanga-zangar lumana kan matsin rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki.

 

Atiku ya yi wannan kakkausar lafazi ne yayin da ake ci gaba da gudanar da zanga-zangar matsin rayuwa a Nijeriya inda wasu jihohi aka samu hargitsi tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar kamar Kano da Abuja.

  • Yanzu Ne Lokacin Da Ya Dace Arsenal Ta Lashe Kofin Firimiya – Kroenke
  • Gwamnatin Kano Ta Sassauta Dokar Hana Fita

Zanga-zangar wacce aka shirya gudanarwa daga 1 zuwa 10 ga watan Agusta, an samu rahotannin asarar rayuka, lalatawa tare da wawure dukiyar gwamnati da al’ummar kasa a wasu jihohin kasar.

Atiku ya bayyana matakin jami’an tsaro na yin amfani da harsashi akan masu zanga-zangar da cewa, “abu ne mai muni da ya yi kama da zamanin mulkin kama-karya na soji.”

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

 

Ya kara da cewa, “Yana da matukar muhimmanci a tunatar da gwamnati da hukumomin tsaro babban hakkin da ya rataya akansu na tabbatar da tsaro ta yadda ‘yan kasa za su iya amfani da ‘yancinsu na yin zanga-zanga ba tare da tsoro ba.

 

“Duk lokacin da jami’an tsaro suka bude wuta kan masu zanga-zangar lumana, babu abinda zai biyo baya face kara ta’azzarar hargitsi.

 

“Ina kira ga kasashen duniya da suka hada da Majalisar Dinkin Duniya da kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa da su sanya ido sosai kan al’amuran da ke faruwa a Nijeriya.

 

“Ina sake jaddada shawarara ga masu zanga-zangar da su dage da yin amfani da ‘yancinsu na yin zanga-zangar lumana tare da yin watsi da duk wani nau’i na tashin hankali.

 

“Amma ya zama dole a gurfanar da masu wawure dukiyar jama’a da barnata kadarorin gwamnati a gaban kotu kamar yadda doka ta tanada, don irin waɗannan ayyukan, suna lalata halaccin zanga-zangar.

 

“Dole ne Shugaba Tinubu ya nuna jagoranci na gaskiya ta hanyar yin gaggawa da aiwatar da bukatun al’ummar Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Matsin RayuwaTabarbarewar Tattalin ArzikiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu Ne Lokacin Da Ya Dace Arsenal Ta Lashe Kofin Firimiya – Kroenke

Next Post

Gwamnati Ta Bai Wa Gwamnoni Fiye Da Naira Biliyan 570 Don Tallafa Wa Talakawa – Tinubu 

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

7 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

11 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

17 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

21 hours ago
Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 
Manyan Labarai

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

2 days ago
Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50
Manyan Labarai

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

2 days ago
Next Post
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu

Gwamnati Ta Bai Wa Gwamnoni Fiye Da Naira Biliyan 570 Don Tallafa Wa Talakawa - Tinubu 

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.