• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Sheikh Muhajjadina Ya Nemi Gwamnati Ta Gaggauta Daukar Mataki

by Bello Hamza
2 years ago
Rayuwa

A daidai lokacin da al’umma Nijeriya ke fama da hauhawar farashin kayyakin abinci da tsadar rayuwa, sanannen malamin addinin nan na Jihar Kano, Sheikh Mujajjadina Sani Kano, wanda kuma shi ne shugaban masu ilimin taurari na Afirka, ya yi kira ga shugabanni a dukkan matakan gwamnati da su gaggauta daukar matakin kawo wa mutane saukin matsin rayuwar da suke fuskanta in har suna son kauce wa fushin Allah (SWT).

Sheikh Muhajjadina ya yi wannan bayanin ne a hirarsa da manema labarai a garin Kano ranar Talata. Ya kuma kara da cewa, halin da mutaten ke ciki da matsin rayuwa ya wuce duk yadda ake tunani. “Lamarin a halin yanzu ya kai matsayin Innalillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun”. Ya ce, babu wani bangare na rayuwar al’umma da ba su dandan wannan halin da ake ciki. A kan haka malaman addini musulmunci da na addnin Kirista suka hadu a yin kira ga gwamnati ta samar wa al’umma mafita.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Sake Lalata Layukan Wutar Lantarki Mai Karfin 330KVA A Yobe
  • Muna Kara Kira Da Ayi Gwajin Kwayoyi Kafin Yin Aure – Marwa

Shehin malamin wanda shi ne shugaban Gidauniyar (Muhajjadina Humanitarian Foundation) wadda ta shahara wajen tallafa wa al’umma, ya kara da cewa, a kullum suna samun mutane masu neman taimako maza da mata da marayu masu lalulori daban-daban., “ Yanzu kusan kowa ka gani a hanya yana bukatar taimako” in ji shi.

Ya kuma ce, mataki mai muhimmanci da ya kamata gwamnati ta dauka don kawo karshen matsalar tsadar rayuwa shi ne dawo da tallafin man fetur da wannan gwamnatin ta janye a farkon kama mulkinta Ya ce, man fetur ya shafi dukkan bangarorin rauwar al’umma, janye shi ya haifar da tsadar rayuwa. Kuma gashi darajar naira na kara faduwa a kullum, “In har gwamnati ta dawo da wadannan abubuwan biyu to da yardar Allah abubuwa za su yi sauki” in ji shi.

Daga nan Shekih Muhajjadina ya yi gargadin cewa, in har gwamnati ba ta dauki matakin kawo wa al’umma saukin rayuwa ba, to lallai za su gamu da fushin Allah (SWT). “Allah na iya kwace mulkin ya ba wadanda za su taimaka wa mutane” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Ya kuma nemi gwamnati a dukkan mataki su nemi shawarwarin malaman addini wajen gudanar da harkokinsu, musamman abin da ya shafi raba wa al’umma tallafi, “Domin daga cikin malamai ne ake da tabbacin samun masu tsoron Allah, wadanda za su jagoranci raba wsa mutane abin da aka tanada, ya kuma kamata a cire duk wani na’u’i na siyasa a wajen bayar da tallafi, domin yunwa bai san banbanci a tsakanin dan APC ko dan PDP ba” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Asuu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro
Labarai

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
majalisar kasa
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
Next Post
Yawan Marasa Aikin Yi A Nijeriya Ya Karu Da Kaso 5 A Karshen 2023 – NBS

Yawan Marasa Aikin Yi A Nijeriya Ya Karu Da Kaso 5 A Karshen 2023 – NBS

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.