ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Sheikh Muhajjadina Ya Nemi Gwamnati Ta Gaggauta Daukar Mataki

by Bello Hamza
2 years ago
Rayuwa

A daidai lokacin da al’umma Nijeriya ke fama da hauhawar farashin kayyakin abinci da tsadar rayuwa, sanannen malamin addinin nan na Jihar Kano, Sheikh Mujajjadina Sani Kano, wanda kuma shi ne shugaban masu ilimin taurari na Afirka, ya yi kira ga shugabanni a dukkan matakan gwamnati da su gaggauta daukar matakin kawo wa mutane saukin matsin rayuwar da suke fuskanta in har suna son kauce wa fushin Allah (SWT).

Sheikh Muhajjadina ya yi wannan bayanin ne a hirarsa da manema labarai a garin Kano ranar Talata. Ya kuma kara da cewa, halin da mutaten ke ciki da matsin rayuwa ya wuce duk yadda ake tunani. “Lamarin a halin yanzu ya kai matsayin Innalillahi Wa Inna Ilaihi Rajiun”. Ya ce, babu wani bangare na rayuwar al’umma da ba su dandan wannan halin da ake ciki. A kan haka malaman addini musulmunci da na addnin Kirista suka hadu a yin kira ga gwamnati ta samar wa al’umma mafita.

  • ‘Yan Boko Haram Sun Sake Lalata Layukan Wutar Lantarki Mai Karfin 330KVA A Yobe
  • Muna Kara Kira Da Ayi Gwajin Kwayoyi Kafin Yin Aure – Marwa

Shehin malamin wanda shi ne shugaban Gidauniyar (Muhajjadina Humanitarian Foundation) wadda ta shahara wajen tallafa wa al’umma, ya kara da cewa, a kullum suna samun mutane masu neman taimako maza da mata da marayu masu lalulori daban-daban., “ Yanzu kusan kowa ka gani a hanya yana bukatar taimako” in ji shi.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ce, mataki mai muhimmanci da ya kamata gwamnati ta dauka don kawo karshen matsalar tsadar rayuwa shi ne dawo da tallafin man fetur da wannan gwamnatin ta janye a farkon kama mulkinta Ya ce, man fetur ya shafi dukkan bangarorin rauwar al’umma, janye shi ya haifar da tsadar rayuwa. Kuma gashi darajar naira na kara faduwa a kullum, “In har gwamnati ta dawo da wadannan abubuwan biyu to da yardar Allah abubuwa za su yi sauki” in ji shi.

Daga nan Shekih Muhajjadina ya yi gargadin cewa, in har gwamnati ba ta dauki matakin kawo wa al’umma saukin rayuwa ba, to lallai za su gamu da fushin Allah (SWT). “Allah na iya kwace mulkin ya ba wadanda za su taimaka wa mutane” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

Ya kuma nemi gwamnati a dukkan mataki su nemi shawarwarin malaman addini wajen gudanar da harkokinsu, musamman abin da ya shafi raba wa al’umma tallafi, “Domin daga cikin malamai ne ake da tabbacin samun masu tsoron Allah, wadanda za su jagoranci raba wsa mutane abin da aka tanada, ya kuma kamata a cire duk wani na’u’i na siyasa a wajen bayar da tallafi, domin yunwa bai san banbanci a tsakanin dan APC ko dan PDP ba” in ji shi.

Rayuwa
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Yawan Marasa Aikin Yi A Nijeriya Ya Karu Da Kaso 5 A Karshen 2023 – NBS

Yawan Marasa Aikin Yi A Nijeriya Ya Karu Da Kaso 5 A Karshen 2023 – NBS

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.