• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

by Sani Anwar
2 years ago
Rayuwa

Duk wanda ya kwana ya tashi a wannan kasa, yana cike da sanin yadda tsadar rayuwa ke ci gaba da ta’azzara, musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci da sauran kayan masarufi.

A kullum ta Allah, idan magidanci ya je kasuwa; sai ya yi kamar ya sa hannu a ka ya ce wayyo Allah, sakamakon farashin yau daban na gobe daban.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

Yana da matukar wuya a cikin irin wannan hali da ake ciki a samu magidancin da ya ke iya dora tukunya a gidansa sau uku a rana, ko da kuwa an samu damar dora tukunyar, watakila sau biyu ne ko sau daya.

Akwai magidanta da dama da suke sanya wa almajirai kwano a gidajensu, a ba su abinci da safe da rana da kuma dare, amma wannan hali da aka tsinci kai a ciki; ya dagula al’amura baki-daya.

Domin kuwa a yanzu, kusan kowa takansa ya ke yi, an koma halin nafsi-nafsi; wanda ko shakka babu Almajirai masu Allah ya ba ku mu samu, suna matukar dandana kudarsu.

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Al’amarin da ya sa Almajiran suka gane cewa, lallai yanzu fa al’amuran sun canza, wannan kuma ya fara ne tun daga 29 ga Mayun 2023, bayan da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya cire tallafin mai, ba tare da wani bata lokaci ba farashin kaya ya fara tashi, tun ana ganin abin kamar wasa, har aka kawo wannan hali da ake ciki yanzu, domin kuwa kullum farashin kara tashin gwauron zabo ya ke yi.

Shi yasa Almajirai abin ya yi musu matukar wuya, su ma suke ji a jikinsu; musamman wadanda a da idan an ba su sadakar abincin da bai yi musu ba, kamar tuwo da sauransu sai su samu gefen kwata su zubar.

Guda daga cikin ire-iren wadannan Almajirai da abokansa suke tuna masa da irin wulakancin da suka rika yi wa tuwo a ‘yan shekarun da suka gabata, fashewa ya yi da kuka, inda su da kansu suke alakanta wulakancin da suka yi wa abincin da kuma wannan hali da suka samu kansu na rashin samun abincin akai-akai a halin yanzu a ciki.

Hausawa na fadin cewa, duk bakin da Allah ya tsaga; ba ya hana shi abinci ko da kuwa babu dadi. Wannan magana ta Bahaushe, ko shakka babu; haka ta ke babu wani gyara a ciki, domin kuwa ba mutum ba ko dabbar da Allah ya halitta, ba ya hana ta abin da za ta kai baki.

Har ila yau, wannan tsadar rayuwa da ake fama da ita, ya sa wasu daga cikin jihohi; musamman a Arewa, fara yin bore ta hanyar aiwatar da zanga-zanga, domin nuna rashin amincewarsu da halin da suka tsinci kansu a ciki.

Koda-yake, a hannu guda kuma, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya nuna damuwarsa tare da sanya dokar ta-baci, a kan harkokin noma; inda gwamnatinsa ta sha alwashin sama wa ‘yan Nijeriya wadataccen abinci, ta yadda har sai an samu rarar da za a rika fita da shi zuwa kasashen waje.

Haka nan, su ma gwamnoni daga jihohi daban-daban, sun yi yunkurin daukar matakai; musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci, duk dai don rage wa al’umma radadin wannan hali da suke ciki.

A nan, muna sake yin kira ga gwamnatin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi da su sake jajircewa tare da mayar da hankali a kan wadannan matsaloli da ke addabar wannan kasa tun kafin kan talakawa ya kwace, su fito su fara yin abin da ba shikenan ba.

Dalili kuwa shi ne, akwai wadanda su ke ganin cewa, duk duniya babu wanda ya kai talakan  Nijeriya hakuri da juriya, domin kuwa ya jure rashin wutar lantarki da rashin hanyoyi da matsalar lafiya da ilimi da ruwan sha da sauran makamantansu, amma ga dukkan alamu an kusa zuwa inda hakurin nasa zai tike.

Saboda haka, yanzu dai shawara ta rage ga mai shiga rijiya, ko dai gwamnati ta yi abin da ya dace, ko kuma a nan gaba ta yi kuka da kanta. Domin kuwa, duk wanda zai sha inuwar gemu; bai kai makogwaro ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Next Post
Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.