ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

by Sani Anwar
2 years ago
Rayuwa

Duk wanda ya kwana ya tashi a wannan kasa, yana cike da sanin yadda tsadar rayuwa ke ci gaba da ta’azzara, musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci da sauran kayan masarufi.

A kullum ta Allah, idan magidanci ya je kasuwa; sai ya yi kamar ya sa hannu a ka ya ce wayyo Allah, sakamakon farashin yau daban na gobe daban.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

Yana da matukar wuya a cikin irin wannan hali da ake ciki a samu magidancin da ya ke iya dora tukunya a gidansa sau uku a rana, ko da kuwa an samu damar dora tukunyar, watakila sau biyu ne ko sau daya.

ADVERTISEMENT

Akwai magidanta da dama da suke sanya wa almajirai kwano a gidajensu, a ba su abinci da safe da rana da kuma dare, amma wannan hali da aka tsinci kai a ciki; ya dagula al’amura baki-daya.

Domin kuwa a yanzu, kusan kowa takansa ya ke yi, an koma halin nafsi-nafsi; wanda ko shakka babu Almajirai masu Allah ya ba ku mu samu, suna matukar dandana kudarsu.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Al’amarin da ya sa Almajiran suka gane cewa, lallai yanzu fa al’amuran sun canza, wannan kuma ya fara ne tun daga 29 ga Mayun 2023, bayan da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya cire tallafin mai, ba tare da wani bata lokaci ba farashin kaya ya fara tashi, tun ana ganin abin kamar wasa, har aka kawo wannan hali da ake ciki yanzu, domin kuwa kullum farashin kara tashin gwauron zabo ya ke yi.

Shi yasa Almajirai abin ya yi musu matukar wuya, su ma suke ji a jikinsu; musamman wadanda a da idan an ba su sadakar abincin da bai yi musu ba, kamar tuwo da sauransu sai su samu gefen kwata su zubar.

Guda daga cikin ire-iren wadannan Almajirai da abokansa suke tuna masa da irin wulakancin da suka rika yi wa tuwo a ‘yan shekarun da suka gabata, fashewa ya yi da kuka, inda su da kansu suke alakanta wulakancin da suka yi wa abincin da kuma wannan hali da suka samu kansu na rashin samun abincin akai-akai a halin yanzu a ciki.

Hausawa na fadin cewa, duk bakin da Allah ya tsaga; ba ya hana shi abinci ko da kuwa babu dadi. Wannan magana ta Bahaushe, ko shakka babu; haka ta ke babu wani gyara a ciki, domin kuwa ba mutum ba ko dabbar da Allah ya halitta, ba ya hana ta abin da za ta kai baki.

Har ila yau, wannan tsadar rayuwa da ake fama da ita, ya sa wasu daga cikin jihohi; musamman a Arewa, fara yin bore ta hanyar aiwatar da zanga-zanga, domin nuna rashin amincewarsu da halin da suka tsinci kansu a ciki.

Koda-yake, a hannu guda kuma, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya nuna damuwarsa tare da sanya dokar ta-baci, a kan harkokin noma; inda gwamnatinsa ta sha alwashin sama wa ‘yan Nijeriya wadataccen abinci, ta yadda har sai an samu rarar da za a rika fita da shi zuwa kasashen waje.

Haka nan, su ma gwamnoni daga jihohi daban-daban, sun yi yunkurin daukar matakai; musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci, duk dai don rage wa al’umma radadin wannan hali da suke ciki.

A nan, muna sake yin kira ga gwamnatin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi da su sake jajircewa tare da mayar da hankali a kan wadannan matsaloli da ke addabar wannan kasa tun kafin kan talakawa ya kwace, su fito su fara yin abin da ba shikenan ba.

Dalili kuwa shi ne, akwai wadanda su ke ganin cewa, duk duniya babu wanda ya kai talakan  Nijeriya hakuri da juriya, domin kuwa ya jure rashin wutar lantarki da rashin hanyoyi da matsalar lafiya da ilimi da ruwan sha da sauran makamantansu, amma ga dukkan alamu an kusa zuwa inda hakurin nasa zai tike.

Saboda haka, yanzu dai shawara ta rage ga mai shiga rijiya, ko dai gwamnati ta yi abin da ya dace, ko kuma a nan gaba ta yi kuka da kanta. Domin kuwa, duk wanda zai sha inuwar gemu; bai kai makogwaro ba.

Rayuwa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.