ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa: Yadda Lamarin Ke Rincabe Wa Almajira Da Mabarata

by Sani Anwar
2 years ago
Rayuwa

Duk wanda ya kwana ya tashi a wannan kasa, yana cike da sanin yadda tsadar rayuwa ke ci gaba da ta’azzara, musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci da sauran kayan masarufi.

A kullum ta Allah, idan magidanci ya je kasuwa; sai ya yi kamar ya sa hannu a ka ya ce wayyo Allah, sakamakon farashin yau daban na gobe daban.

  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Majalisar Gudanarwar Kasar 
  • Zaben Fitar Da Gwani Na APC A Edo Ya Bar Baya Da Kura

Yana da matukar wuya a cikin irin wannan hali da ake ciki a samu magidancin da ya ke iya dora tukunya a gidansa sau uku a rana, ko da kuwa an samu damar dora tukunyar, watakila sau biyu ne ko sau daya.

ADVERTISEMENT

Akwai magidanta da dama da suke sanya wa almajirai kwano a gidajensu, a ba su abinci da safe da rana da kuma dare, amma wannan hali da aka tsinci kai a ciki; ya dagula al’amura baki-daya.

Domin kuwa a yanzu, kusan kowa takansa ya ke yi, an koma halin nafsi-nafsi; wanda ko shakka babu Almajirai masu Allah ya ba ku mu samu, suna matukar dandana kudarsu.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Al’amarin da ya sa Almajiran suka gane cewa, lallai yanzu fa al’amuran sun canza, wannan kuma ya fara ne tun daga 29 ga Mayun 2023, bayan da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya cire tallafin mai, ba tare da wani bata lokaci ba farashin kaya ya fara tashi, tun ana ganin abin kamar wasa, har aka kawo wannan hali da ake ciki yanzu, domin kuwa kullum farashin kara tashin gwauron zabo ya ke yi.

Shi yasa Almajirai abin ya yi musu matukar wuya, su ma suke ji a jikinsu; musamman wadanda a da idan an ba su sadakar abincin da bai yi musu ba, kamar tuwo da sauransu sai su samu gefen kwata su zubar.

Guda daga cikin ire-iren wadannan Almajirai da abokansa suke tuna masa da irin wulakancin da suka rika yi wa tuwo a ‘yan shekarun da suka gabata, fashewa ya yi da kuka, inda su da kansu suke alakanta wulakancin da suka yi wa abincin da kuma wannan hali da suka samu kansu na rashin samun abincin akai-akai a halin yanzu a ciki.

Hausawa na fadin cewa, duk bakin da Allah ya tsaga; ba ya hana shi abinci ko da kuwa babu dadi. Wannan magana ta Bahaushe, ko shakka babu; haka ta ke babu wani gyara a ciki, domin kuwa ba mutum ba ko dabbar da Allah ya halitta, ba ya hana ta abin da za ta kai baki.

Har ila yau, wannan tsadar rayuwa da ake fama da ita, ya sa wasu daga cikin jihohi; musamman a Arewa, fara yin bore ta hanyar aiwatar da zanga-zanga, domin nuna rashin amincewarsu da halin da suka tsinci kansu a ciki.

Koda-yake, a hannu guda kuma, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya nuna damuwarsa tare da sanya dokar ta-baci, a kan harkokin noma; inda gwamnatinsa ta sha alwashin sama wa ‘yan Nijeriya wadataccen abinci, ta yadda har sai an samu rarar da za a rika fita da shi zuwa kasashen waje.

Haka nan, su ma gwamnoni daga jihohi daban-daban, sun yi yunkurin daukar matakai; musamman a bangaren da ya shafi kayan abinci, duk dai don rage wa al’umma radadin wannan hali da suke ciki.

A nan, muna sake yin kira ga gwamnatin tarayya, jihohi da kuma kananan hukumomi da su sake jajircewa tare da mayar da hankali a kan wadannan matsaloli da ke addabar wannan kasa tun kafin kan talakawa ya kwace, su fito su fara yin abin da ba shikenan ba.

Dalili kuwa shi ne, akwai wadanda su ke ganin cewa, duk duniya babu wanda ya kai talakan  Nijeriya hakuri da juriya, domin kuwa ya jure rashin wutar lantarki da rashin hanyoyi da matsalar lafiya da ilimi da ruwan sha da sauran makamantansu, amma ga dukkan alamu an kusa zuwa inda hakurin nasa zai tike.

Saboda haka, yanzu dai shawara ta rage ga mai shiga rijiya, ko dai gwamnati ta yi abin da ya dace, ko kuma a nan gaba ta yi kuka da kanta. Domin kuwa, duk wanda zai sha inuwar gemu; bai kai makogwaro ba.

Rayuwa
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tinubu Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Kan Jajircewarsu Wajen Kawo Karshen Ta’addanci

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

Rikita-rikitar ‘Yar Tiktok Murja Kunya Da Hukumar Hisba A Kano

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.