• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftar Muhalli: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Domin Tsaftace Jihar Zamfara

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Tsaftar Muhalli: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Domin Tsaftace Jihar Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da ɗorewar tsaftar muhalli da manufofin ƙarfafa al’umma su rungumi al’adar tsafta a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne gwamnan ya ƙaddamar da rabon motoci da kayayyakin aiki daban-daban na shirin Tsaftar Muhalli na Matasan Zamfara a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon kayayyakin wani babban tsari ne na shirin Tsaftace Jihar Zamfara, wanda ya haɗa da manyan motocin kwasar shara guda goma, injinan shara guda huɗu, manyan motoci guda biyu, da babura 65.

 

Labarai Masu Nasaba

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

Sanarwar ta ƙara da cewa, shirin na ‘Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes’ (ACReSAL) ya samar da kwandon shara guda 450 na ma’aikatun gwamnati da kuma kwandon shara na ƙarfe 55 ga al’ummomin birane.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa tsaftataccen muhalli yana jawo jari, da bunƙasa harkokin yawon buɗe ido, da inganta rayuwar al’ummar jihar Zamfara baki ɗaya.

 

“Wannan taron ya nuna wani gagarumin ci gaba a ƙoƙarinmu na ceto jihar Zamfara cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“Shirin ƙarfafa matasa na Zamfara an yi shi ne don ƙarfafa matasanmu masu kuzari da hazaƙa ta hanyar shigar da su cikin ayyuka masu ma’ana don inganta tsaftar muhalli a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri ya wuce inganta tsaftar muhalli kaɗai; yana ba da guraben ayyukan yi da haɓaka dabarun kasuwanci. Muna fatan cewa ta hanyar shiga cikin waɗannan shirye-shirye, matasanmu za su sami ƙwarewa sosai da kuma fahimtar alhakin hidimta wa al’umma.

 

“Ta hanyar shirin ZAYOSAP, muna kuma saka hannun jari a makomar matasanmu. Muna ba su kayan aiki masu muhimmanci da ilimin da zai shirya su don zama shugabanni da wakilai wajen kawo sauyi a al’ummominsu. Wannan cikakkiyar dabara ta ƙarfafa matasa da ɗorewar muhalli ba shakka za ta haifar da fa’ida ga jiharmu.

 

“Yayin da muke ƙaddamar da wannan shirin a yau, mun kafa tarihi ne ga al’umma masu zuwa. Ina fata wannan shiri zai zama abin koyi ga wasu jihohi uku da zaburar da saura wajen ƙirƙirar irin wannan shiri a faɗin Nijeriya.

 

“A bayyane yake cewa yayin da muke gina muhimman ababen more rayuwa a faɗin jihar, tsaftar muhalli na da matuƙar muhimmanci ga ɗorewar rayuwar al’umma da kuma gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Tsaftace tituna, kasuwanni, da wuraren jama’a suna nuna kimar al’umma a idon duniya. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da suka haɗa da shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, da ɗaukacin al’ummarmu da su goyi bayan wannan shiri ta hanyar rungumar al’adar tsafta.

 

“Da waɗannan kalamai, nake farin cikin ƙaddamar da shirin tallafa wa matasan Zamfara a hukumance. Ina kira ga al’ummar jiharmu da su bai wa wannan shiri goyon baya tare da haɗa kai domin cimma burin jihar Zamfara na tsafta, lafiya da wadata.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Kara Sabbin Guraben Aikin Yi A Birane Miliyan 12.56 A Shekarar 2024

Next Post

Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

3 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

17 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

20 hours ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

22 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

23 hours ago
Next Post
Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.