ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftar Muhalli: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Domin Tsaftace Jihar Zamfara

by Sulaiman
2 years ago
Tsaftar muhalli

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da ɗorewar tsaftar muhalli da manufofin ƙarfafa al’umma su rungumi al’adar tsafta a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne gwamnan ya ƙaddamar da rabon motoci da kayayyakin aiki daban-daban na shirin Tsaftar Muhalli na Matasan Zamfara a gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon kayayyakin wani babban tsari ne na shirin Tsaftace Jihar Zamfara, wanda ya haɗa da manyan motocin kwasar shara guda goma, injinan shara guda huɗu, manyan motoci guda biyu, da babura 65.

 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Sanarwar ta ƙara da cewa, shirin na ‘Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes’ (ACReSAL) ya samar da kwandon shara guda 450 na ma’aikatun gwamnati da kuma kwandon shara na ƙarfe 55 ga al’ummomin birane.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa tsaftataccen muhalli yana jawo jari, da bunƙasa harkokin yawon buɗe ido, da inganta rayuwar al’ummar jihar Zamfara baki ɗaya.

 

“Wannan taron ya nuna wani gagarumin ci gaba a ƙoƙarinmu na ceto jihar Zamfara cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“Shirin ƙarfafa matasa na Zamfara an yi shi ne don ƙarfafa matasanmu masu kuzari da hazaƙa ta hanyar shigar da su cikin ayyuka masu ma’ana don inganta tsaftar muhalli a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri ya wuce inganta tsaftar muhalli kaɗai; yana ba da guraben ayyukan yi da haɓaka dabarun kasuwanci. Muna fatan cewa ta hanyar shiga cikin waɗannan shirye-shirye, matasanmu za su sami ƙwarewa sosai da kuma fahimtar alhakin hidimta wa al’umma.

 

“Ta hanyar shirin ZAYOSAP, muna kuma saka hannun jari a makomar matasanmu. Muna ba su kayan aiki masu muhimmanci da ilimin da zai shirya su don zama shugabanni da wakilai wajen kawo sauyi a al’ummominsu. Wannan cikakkiyar dabara ta ƙarfafa matasa da ɗorewar muhalli ba shakka za ta haifar da fa’ida ga jiharmu.

 

“Yayin da muke ƙaddamar da wannan shirin a yau, mun kafa tarihi ne ga al’umma masu zuwa. Ina fata wannan shiri zai zama abin koyi ga wasu jihohi uku da zaburar da saura wajen ƙirƙirar irin wannan shiri a faɗin Nijeriya.

 

“A bayyane yake cewa yayin da muke gina muhimman ababen more rayuwa a faɗin jihar, tsaftar muhalli na da matuƙar muhimmanci ga ɗorewar rayuwar al’umma da kuma gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Tsaftace tituna, kasuwanni, da wuraren jama’a suna nuna kimar al’umma a idon duniya. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da suka haɗa da shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, da ɗaukacin al’ummarmu da su goyi bayan wannan shiri ta hanyar rungumar al’adar tsafta.

 

“Da waɗannan kalamai, nake farin cikin ƙaddamar da shirin tallafa wa matasan Zamfara a hukumance. Ina kira ga al’ummar jiharmu da su bai wa wannan shiri goyon baya tare da haɗa kai domin cimma burin jihar Zamfara na tsafta, lafiya da wadata.”

Tsaftar muhalli
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.