ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftar Muhalli: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Domin Tsaftace Jihar Zamfara

by Sulaiman
1 year ago
Tsaftar muhalli

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da ɗorewar tsaftar muhalli da manufofin ƙarfafa al’umma su rungumi al’adar tsafta a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne gwamnan ya ƙaddamar da rabon motoci da kayayyakin aiki daban-daban na shirin Tsaftar Muhalli na Matasan Zamfara a gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon kayayyakin wani babban tsari ne na shirin Tsaftace Jihar Zamfara, wanda ya haɗa da manyan motocin kwasar shara guda goma, injinan shara guda huɗu, manyan motoci guda biyu, da babura 65.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sanarwar ta ƙara da cewa, shirin na ‘Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes’ (ACReSAL) ya samar da kwandon shara guda 450 na ma’aikatun gwamnati da kuma kwandon shara na ƙarfe 55 ga al’ummomin birane.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa tsaftataccen muhalli yana jawo jari, da bunƙasa harkokin yawon buɗe ido, da inganta rayuwar al’ummar jihar Zamfara baki ɗaya.

 

“Wannan taron ya nuna wani gagarumin ci gaba a ƙoƙarinmu na ceto jihar Zamfara cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“Shirin ƙarfafa matasa na Zamfara an yi shi ne don ƙarfafa matasanmu masu kuzari da hazaƙa ta hanyar shigar da su cikin ayyuka masu ma’ana don inganta tsaftar muhalli a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri ya wuce inganta tsaftar muhalli kaɗai; yana ba da guraben ayyukan yi da haɓaka dabarun kasuwanci. Muna fatan cewa ta hanyar shiga cikin waɗannan shirye-shirye, matasanmu za su sami ƙwarewa sosai da kuma fahimtar alhakin hidimta wa al’umma.

 

“Ta hanyar shirin ZAYOSAP, muna kuma saka hannun jari a makomar matasanmu. Muna ba su kayan aiki masu muhimmanci da ilimin da zai shirya su don zama shugabanni da wakilai wajen kawo sauyi a al’ummominsu. Wannan cikakkiyar dabara ta ƙarfafa matasa da ɗorewar muhalli ba shakka za ta haifar da fa’ida ga jiharmu.

 

“Yayin da muke ƙaddamar da wannan shirin a yau, mun kafa tarihi ne ga al’umma masu zuwa. Ina fata wannan shiri zai zama abin koyi ga wasu jihohi uku da zaburar da saura wajen ƙirƙirar irin wannan shiri a faɗin Nijeriya.

 

“A bayyane yake cewa yayin da muke gina muhimman ababen more rayuwa a faɗin jihar, tsaftar muhalli na da matuƙar muhimmanci ga ɗorewar rayuwar al’umma da kuma gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Tsaftace tituna, kasuwanni, da wuraren jama’a suna nuna kimar al’umma a idon duniya. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da suka haɗa da shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, da ɗaukacin al’ummarmu da su goyi bayan wannan shiri ta hanyar rungumar al’adar tsafta.

 

“Da waɗannan kalamai, nake farin cikin ƙaddamar da shirin tallafa wa matasan Zamfara a hukumance. Ina kira ga al’ummar jiharmu da su bai wa wannan shiri goyon baya tare da haɗa kai domin cimma burin jihar Zamfara na tsafta, lafiya da wadata.”

Tsaftar muhalli
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.