ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaftar Muhalli: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci Domin Tsaftace Jihar Zamfara

by Sulaiman
1 year ago
Tsaftar muhalli

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya bayyana ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da ɗorewar tsaftar muhalli da manufofin ƙarfafa al’umma su rungumi al’adar tsafta a Jihar Zamfara.

 

A ranar Talata ne gwamnan ya ƙaddamar da rabon motoci da kayayyakin aiki daban-daban na shirin Tsaftar Muhalli na Matasan Zamfara a gidan gwamnati da ke Gusau.

ADVERTISEMENT
  • Trump Zai Fuskanci Tirjiya A Duniya, Ba Soyayya Ba – Shehu Sani
  • Matatar Dangote Ta Bai Wa Ɗalibai 473 Tallafin Karatu

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa rabon kayayyakin wani babban tsari ne na shirin Tsaftace Jihar Zamfara, wanda ya haɗa da manyan motocin kwasar shara guda goma, injinan shara guda huɗu, manyan motoci guda biyu, da babura 65.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Sanarwar ta ƙara da cewa, shirin na ‘Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes’ (ACReSAL) ya samar da kwandon shara guda 450 na ma’aikatun gwamnati da kuma kwandon shara na ƙarfe 55 ga al’ummomin birane.

 

A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa tsaftataccen muhalli yana jawo jari, da bunƙasa harkokin yawon buɗe ido, da inganta rayuwar al’ummar jihar Zamfara baki ɗaya.

 

“Wannan taron ya nuna wani gagarumin ci gaba a ƙoƙarinmu na ceto jihar Zamfara cikin watanni 20 da suka gabata.

 

“Shirin ƙarfafa matasa na Zamfara an yi shi ne don ƙarfafa matasanmu masu kuzari da hazaƙa ta hanyar shigar da su cikin ayyuka masu ma’ana don inganta tsaftar muhalli a faɗin jihar.

 

“Wannan shiri ya wuce inganta tsaftar muhalli kaɗai; yana ba da guraben ayyukan yi da haɓaka dabarun kasuwanci. Muna fatan cewa ta hanyar shiga cikin waɗannan shirye-shirye, matasanmu za su sami ƙwarewa sosai da kuma fahimtar alhakin hidimta wa al’umma.

 

“Ta hanyar shirin ZAYOSAP, muna kuma saka hannun jari a makomar matasanmu. Muna ba su kayan aiki masu muhimmanci da ilimin da zai shirya su don zama shugabanni da wakilai wajen kawo sauyi a al’ummominsu. Wannan cikakkiyar dabara ta ƙarfafa matasa da ɗorewar muhalli ba shakka za ta haifar da fa’ida ga jiharmu.

 

“Yayin da muke ƙaddamar da wannan shirin a yau, mun kafa tarihi ne ga al’umma masu zuwa. Ina fata wannan shiri zai zama abin koyi ga wasu jihohi uku da zaburar da saura wajen ƙirƙirar irin wannan shiri a faɗin Nijeriya.

 

“A bayyane yake cewa yayin da muke gina muhimman ababen more rayuwa a faɗin jihar, tsaftar muhalli na da matuƙar muhimmanci ga ɗorewar rayuwar al’umma da kuma gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Tsaftace tituna, kasuwanni, da wuraren jama’a suna nuna kimar al’umma a idon duniya. Ina kira ga masu ruwa da tsaki da suka haɗa da shugabannin al’umma, sarakunan gargajiya, da ɗaukacin al’ummarmu da su goyi bayan wannan shiri ta hanyar rungumar al’adar tsafta.

 

“Da waɗannan kalamai, nake farin cikin ƙaddamar da shirin tallafa wa matasan Zamfara a hukumance. Ina kira ga al’ummar jiharmu da su bai wa wannan shiri goyon baya tare da haɗa kai domin cimma burin jihar Zamfara na tsafta, lafiya da wadata.”

Tsaftar muhalli
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

Sin Da AU Sun Cimma Nasarori A Fannonin Diflomasiyya Da Tattalin Arziki

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.