• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Dangote Da Mahukuntan Fetur: Ina Muka Dosa?

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Labarai, Manyan Labarai
0
Tsakanin Dangote Da Mahukuntan Fetur: Ina Muka Dosa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, rikicin da ya barke na cacar baki tsakanin hamshakin attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote da mahukuntan bangaren mai na Nijeriya ya dauki hankali sosai a manyan gidajen jaridu da sauran kafofin sadarwa har da na sada zumunta.

Saboda mamakin abin, ‘yan Nijeriya masu kishi sun shiga rudani a kan rikicin. Da farko, attajirin ya zargi Kamfanonin Mai na Waje da ke aiki a Nijeriya da yi wa sabuwar matatarsa zagon kasa ta hanyar hana su samun danyen man da ake hakowa a Nijeriya da rahusa. Sai ma ya zama, yadda za a sayar wa wasu a waje ya fi nashi sauki, inda shi aka kara masa farashin daga dala 4 zuwa dala 6 a kan kowace ganga.

  • Majalisa Ta Nemi A Kori Shugaban Hukumar NMDPRA Kan Zargin Rashin Ingancin Matatar Dangote
  • Duk Da Sulhu, Tsugune Ba Ta Kare Ba Tsakanin Dangote Da Mahukuntan Mai

Uhum! In ji mai ciwon hakori. Cikakken Dan Nijeriya, ya kafa matatar mai a kasarsa ta gado amma an ki sayar masa da man kasarsa don ya tace ya sayar wa da ‘yan kasarsa. Wace irin kasa ce wannan? Kuma maimakon mahukuntan da abin ya shafa su nemi hanyoyin daidaita lamarin, sai suka zama masu mara baya ga kamfanonin na waje har ma suka fi su tsanantawa ta hanyar kushe sabuwar matatar man wacce babu irin ta kaf Afirka, alhali kuma sun ki gyara na kasa da ake da su guda uku a Kaduna, Warri da Fatakwal duk da makudan biliyoyin da aka narka.

Lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya cire tallafin mai, ya yi alkawari wa ‘yan kwadago cewa matatar mai ta Fatakwal za ta fara aiki a watan Disambar 2023. Aka ce ba a kammala aiki ba, amma a watan Janairun 2024 za ta fara, da watan ya zo ya shige sai aka kuma cewa babu shakka a watan Afrilu za ta fara, amma mai karatu har yau shiru kamar Malam ya ci shirwa. Kuma wani dan kasuwa shi kadai, ya bugi kirji, ya yi abin da kasar ta kasa yi, amma sai aka rika bin sa da tsangwama da hantara.

Kamar yadda na ji wani mai hikima yana jawabi a wani faifan bidiyo da na gani yana yawo a shafukan sada zumunta yana cewa, Nijeriya ta kasance tana sayar da danyen mai a kasashen waje daga nan sai ta sayo tataccen mai daga can. A yanzu kuma da aka samu matatar mai ta Dangote, sai aka hana matatar man isasshen danyen mai da za ta tace, don haka sai aka kuma garzayawa waje don shigo da danyen mai wadda daga bisani bayan tacewa za a kuma fitarwa zuwa waje. Wannan wane irin kwance zani ne a kasuwa?

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

A duk kasashen Afira, kasashe biyu ne rak ba su shigo da tataccen mai daga waje. Daga Aljeriya sai Libiya, sannan kusan an kwashe shekara 20 kasar Angola tana fafutukar kafa babbar matatar mai abin bai yiwu ba, haka nan ita ma Yuganda ta kwashe shekaru 15, duk dai bai yiwu ba. To, mu me ya sa da namu ya yi maimakon a yaba sai aka koma bita-da-kulli?

Matatar man Dangote abar alfahari ce ga Nijeriya a tsakanin sa’o’inta na duniya. Saboda tun daga zayyanarta har zuwa gina ta da sanya na’urorin aiki komai a Nijeriya aka yi. Na ji cewa, Dangote ya yi wa katafaren gine-gine da ake ganin babu kamarsa a Nijeriya na Julius Berger tayin aikin amma kamfanin ya ce ba shi da kayan aikin da zai iya kwangilar. Dole ta sa Dangoten da kansa ya niki gari ya bazama neman kayan aikinsa da kansa kuma ya yi amfani da injiniyoyi na cikin gida masu yawa wajen aikin ginawa.

Dangote

Kamar yadda mataimakin shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Mista Edwin ya tabbatar, wannan ne karon farko da aka samu katafariyar matatar mai da za ta tace ganga 650,000 a kullum da aka hada kwangilar sauton kayan aiki da kawo su da kuma gina su a lokaci guda a duk fadin duniya kuma irin ta, ta uku da ta hade sassan matatar mai a wuri daya a duk fadin duniya. Wannan kadai bai ishe mu alfahari ba? Sannan Bisa kayan aikin da aka shigo da su na gina matatar, Dangote ya ce babu wani aikin gini da zai iya gagarar Nijeriya a halin yanzu.

Shugaban Hukumar Daidata Al’amuran Mai ta Kasa, Injiniya Faruk Ahmed ya yi zargin Dangote yana yunkuri ne na yin babakere a harkar man Nijeriya, to amma Dangoten ya ba shi amsar cewa, “ba mu taba ko da darsawa a zuciya cewa, mu hana wani yin kasuwancin da muke yi ba. Duk wanda zai yi ai ga fili ga doki.”

Kuma ma don Allah, don dan kasa ya gina wani abu na samun kudi a kasarsa ta gado mene ne na kyashi? Ai da arziki a garin wasu gwara a naku. Amma a wurin shugabannin mai na Nijeriya gwara a bai wa turawan yamma. Shi ya sa wani ya ce, “da zarar wani ya yi maka bayani a game da yadda za ka fahimci Nijeriya, bayan ya kammala sai ka ce ka gane, to tabbas bai yi maka bayani yadda ya kamata ba ne,” ma’ana, duk yadda aka kai ga yi maka bayani, za ka rasa INA MUKA DOSA?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DangoteFetur
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Shiga Rudani Saboda Rashin Isar Tirelolin Shinkafar Tallafi Wasu Jihohi

Next Post

Katsina United Ta Kammala Ɗaukar Ƴan Wasa Biyu Daga Kano Pillars 

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

23 minutes ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya
Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

4 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

5 hours ago
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

17 hours ago
Next Post
Katsina United Ta Kammala Ɗaukar Ƴan Wasa Biyu Daga Kano Pillars 

Katsina United Ta Kammala Ɗaukar Ƴan Wasa Biyu Daga Kano Pillars 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.