• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Kafa Shingaye Da Gina Gada: Yadda Matakan Amurka Da Sin Suka Bambanta Sosai

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Tsakanin Kafa Shingaye Da Gina Gada: Yadda Matakan Amurka Da Sin Suka Bambanta Sosai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ya zuwa wannan shekara, cinikin tsakanin Amurka da Afirka na dogaro ne da dokar AGOA matuka, saboda wannan doka ta bai wa kayayyaki kirar Afirka damar shiga kasuwannin Amurka ba tare da biya harajin kwastam ba. Amma yadda shugaban kasar Amurka Donald Trump ya fara kakkaba wa kasashen da ke huldar ciniki da kasarsa karin haraji, ciki har da kasashen Afirka 51 ka iya haifar da kalubale ga kasuwancin Afirka na fitar da kayayyakinsu zuwa Amurka.

 

Kamfanin dillancin labarai na Rueters ya ba da labari a kwanan baya cewa, manazarta na ganin cewa, dokar AGOA wadda wa’adinta zai kare a watan Satumba mai zuwa na fuskantar kalubalen daina aiki. Kasashen Afirka na fahimtar wannan matsala, inda ministar masana’antu da ciniki da zuba jari ta Najeriya Dr. Jumoke Oduwole ta bayyana a cikin wata sanarwar cewa, “Ko da yake man fetur ya kasance albarkatu mafi muhimmanci da Najeriya ke fitarwa zuwa Amurka, amma akwai wasu kayayyaki da ba na man fetur ba da aka yafe musu haraji bisa dokar AGOA wadda, wadanda kuma za su fuskanci matsala”.

  • Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sabuwar Cibiyar Sayar Da Magunguna Da Ke Damaturu
  • Yawan Wutar Lantarki Da Kasar Sin Ke Iya Samarwa Ya Karu Da Kaso 14.6% Zuwa Karshen Maris Na Bana

Amma kasashen Afirka ba za su zauna kawai sun yi asara bisa wannan yanayi na maras tabbaci ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nahiyar dake da yawan mutane fiye da biliyan 1.4 na da babbar kasuwa. Matakin Donald Trump ka iya samar wa kasashen nahiyar damar karfafa hadin gwiwarsu da inganta tsarin masana’antu. Ban da wannan kuma, kasashen Afirka suna iya samun mafita ta hanyar kara hadin gwiwa da kasashe masu tasowa musamman ma kasar Sin.

 

Cikin shekaru 16 a jere ne Sin take kan matsayin abokiyar ciniki mafi girma ga Afirka. A maimakon matakin da Amurka ke dauka wato kara dora wa kasashen Afirka haraji, Sin tana dukufa kan taka rawar gani cikin tsarin hadin gwiwar mabambantan bangarori da gaggauta hadin gwiwar kasashe masu tasowa da cin moriya tare, matakin da zai samar da yanayi mai dorewa ga bunkasarsu baki daya.

 

Kazalika, ba kamar yadda Amurka ta kakkaba wa kasashen Afirka harajin da yawansa ya kai tsakanin 10% zuwa 50% ba, Sin ta soke dukkan harajin kwastam ne a kan kasashen da suka fi koma baya wadanda suka kulla dangantakar diflomasiyya tsakaninsu da Sin, ciki har da wasu kasashen Afirka 33, matakin da ya samar wa Afirka damammaki masu kyau wajen more manyan kasuwannin Sin.

 

Muna iya gani daga wadannan alkaluma cewa: Wane ne ya dunkula hannu kuma wane ne ya bude hannun runguma?, Wane ne ya kafa shingaye kuma wane ne ya gina gada? Girman kai da matukar son kai na zubar da mutumcin da kimar Amurka, yayin da kuma a maimakon haka, kuma matakin bude kofa da hadin gwiwa da Sin ke dauka na kara bayyana nagartaccen mutumci da martabar kasar. (MINA)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Inganta Kiwon Lafiya: Gwamna Buni Ya Ziyarci Sashen Koyar Da Kwararrun Likitoci A Damaturu

Next Post

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababbun Shugabannin Gabon Da Ecuador

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

2 days ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

4 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

1 week ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

1 week ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

2 weeks ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababbun Shugabannin Gabon Da Ecuador

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Zababbun Shugabannin Gabon Da Ecuador

LABARAI MASU NASABA

Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.