• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hausawa suna da wani karin magana mai ban sha’awa da ke kara shaja’antar da mazumunta a kan kara dankon zumunci a tsakaninsu, shi ne “zumunta a kafa take”.

Yayin da sabuwar shekarar 2025 ta fara lulawa, kasar Sin ta fara sauke hakkinta na yaukaka zumunci a tsakaninta da nahiyar Afirka ta hanyar fara ziyarar ministan harkokinta na waje, Wang Yi a wasu kasashe hudu na nahiyar da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da kuma Nijeriya.

  • An Kashe ’Yan Ta’adda 34 Da Sojoji 6 A Harin Borno – Shalkwatar Tsaro
  • Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Ziyarar ta kasance wani bangare na fara shirye-shiryen aiwatar da tsare-tsare 10 da Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi wa nahiyar Afirka albishir da su a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a watan Satumban bara.

Sin da Afirka sun yanke shawarar daga matsayin dangantakarsu zuwa kololuwa da za ta karade dukkan fannoni na ci gaba a sabon zamani. Wannan zumunci yana ci gaba da haifar da da mai ido saboda yadda ake gudanar da harkoki a karkashinsa bisa gaskiya da amana ba tare da kumbiya-kumbiya ba. Inda hakan ya taimaka ga raya ababen more rayuwa a Afirka.

Cikin shekaru 25 da suka gabata kacal, kamfanonin kasar Sin da suka zuba jari a nahiyar Afirka sun taimaka wa kasashen yankin da ginawa ko kara inganta sufurin jirgin kasa da ya kunshi layukan dogo fiye da kilomita 10,000, da manyan tituna da tsawonsu ya kai kusan kilomita 100,000, da gina manyan gadoji kimanin 1,000, baya ga tasoshin jiragen ruwa ciki har da masu zurfin ruwa da adadinsu ya kai 100, kana da habaka samar da wutar lantarki ta hanyar gina tasoshin janyowa da layukan rarrabawa da a kalla za su kai tsawon kilomita 66,000.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Kasar Sin ta kuma himmatu wajen tallafa wa Afirka wajen gina masana’antu da za su rika sarrafa ko san’anta kayayyaki a cikin gida domin taimaka wa habakar tattalin arzikin yankin. Haka nan a bangaren ci gaban kimiyya da fasaha da aiki da sabbin makamashi marasa gurbata muhalli, kana bangaren aikin gona ma ba a bar shi a baya ba.

A tsakanin shekarun da ba su wuce 10 ba, kasar Sin ta gina cibiyoyin inganta fasahar aikin gona guda 24 a sassan Afirka tare da habaka fasahohin aikin gona daban-daban fiye da 300 wanda hakan ya taimaka gaya ga samun girbi mai albarka da a kalla kashi 30 zuwa 60 cikin dari inda manoma kimanin miliyan daya suka ci gajiyar abin.

Irin wannan zumunci ake so ya dawwama ana sadar da shi saboda kamar yadda Hausawa kan ce “na ji dadi shi ne batu, ba na saba ba!”(Abdulrazaq Yahuza Jere)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

Next Post

Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

Related

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

12 minutes ago
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere
Daga Birnin Sin

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

1 hour ago
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

2 hours ago
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa
Daga Birnin Sin

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

4 hours ago
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

1 day ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

1 day ago
Next Post
Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.