ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

Hausawa suna da wani karin magana mai ban sha’awa da ke kara shaja’antar da mazumunta a kan kara dankon zumunci a tsakaninsu, shi ne “zumunta a kafa take”.

Yayin da sabuwar shekarar 2025 ta fara lulawa, kasar Sin ta fara sauke hakkinta na yaukaka zumunci a tsakaninta da nahiyar Afirka ta hanyar fara ziyarar ministan harkokinta na waje, Wang Yi a wasu kasashe hudu na nahiyar da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da kuma Nijeriya.

  • An Kashe ’Yan Ta’adda 34 Da Sojoji 6 A Harin Borno – Shalkwatar Tsaro
  • Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Ziyarar ta kasance wani bangare na fara shirye-shiryen aiwatar da tsare-tsare 10 da Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi wa nahiyar Afirka albishir da su a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a watan Satumban bara.

ADVERTISEMENT

Sin da Afirka sun yanke shawarar daga matsayin dangantakarsu zuwa kololuwa da za ta karade dukkan fannoni na ci gaba a sabon zamani. Wannan zumunci yana ci gaba da haifar da da mai ido saboda yadda ake gudanar da harkoki a karkashinsa bisa gaskiya da amana ba tare da kumbiya-kumbiya ba. Inda hakan ya taimaka ga raya ababen more rayuwa a Afirka.

Cikin shekaru 25 da suka gabata kacal, kamfanonin kasar Sin da suka zuba jari a nahiyar Afirka sun taimaka wa kasashen yankin da ginawa ko kara inganta sufurin jirgin kasa da ya kunshi layukan dogo fiye da kilomita 10,000, da manyan tituna da tsawonsu ya kai kusan kilomita 100,000, da gina manyan gadoji kimanin 1,000, baya ga tasoshin jiragen ruwa ciki har da masu zurfin ruwa da adadinsu ya kai 100, kana da habaka samar da wutar lantarki ta hanyar gina tasoshin janyowa da layukan rarrabawa da a kalla za su kai tsawon kilomita 66,000.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Kasar Sin ta kuma himmatu wajen tallafa wa Afirka wajen gina masana’antu da za su rika sarrafa ko san’anta kayayyaki a cikin gida domin taimaka wa habakar tattalin arzikin yankin. Haka nan a bangaren ci gaban kimiyya da fasaha da aiki da sabbin makamashi marasa gurbata muhalli, kana bangaren aikin gona ma ba a bar shi a baya ba.

A tsakanin shekarun da ba su wuce 10 ba, kasar Sin ta gina cibiyoyin inganta fasahar aikin gona guda 24 a sassan Afirka tare da habaka fasahohin aikin gona daban-daban fiye da 300 wanda hakan ya taimaka gaya ga samun girbi mai albarka da a kalla kashi 30 zuwa 60 cikin dari inda manoma kimanin miliyan daya suka ci gajiyar abin.

Irin wannan zumunci ake so ya dawwama ana sadar da shi saboda kamar yadda Hausawa kan ce “na ji dadi shi ne batu, ba na saba ba!”(Abdulrazaq Yahuza Jere)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara
  • Sulaiman
    Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan
  • Sulaiman
    ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
  • Sulaiman
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.