ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsakanin Sin Da Afirka: Zumunta A Kafa Take

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

Hausawa suna da wani karin magana mai ban sha’awa da ke kara shaja’antar da mazumunta a kan kara dankon zumunci a tsakaninsu, shi ne “zumunta a kafa take”.

Yayin da sabuwar shekarar 2025 ta fara lulawa, kasar Sin ta fara sauke hakkinta na yaukaka zumunci a tsakaninta da nahiyar Afirka ta hanyar fara ziyarar ministan harkokinta na waje, Wang Yi a wasu kasashe hudu na nahiyar da suka hada da Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da kuma Nijeriya.

  • An Kashe ’Yan Ta’adda 34 Da Sojoji 6 A Harin Borno – Shalkwatar Tsaro
  • Éric Chelle Ya Zama Sabon Kocin Super Eagles

Ziyarar ta kasance wani bangare na fara shirye-shiryen aiwatar da tsare-tsare 10 da Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya yi wa nahiyar Afirka albishir da su a taron koli na dandalin hadin gwiwar Sin da Afirka, watau FOCAC da ya gudana a birnin Beijing a watan Satumban bara.

ADVERTISEMENT

Sin da Afirka sun yanke shawarar daga matsayin dangantakarsu zuwa kololuwa da za ta karade dukkan fannoni na ci gaba a sabon zamani. Wannan zumunci yana ci gaba da haifar da da mai ido saboda yadda ake gudanar da harkoki a karkashinsa bisa gaskiya da amana ba tare da kumbiya-kumbiya ba. Inda hakan ya taimaka ga raya ababen more rayuwa a Afirka.

Cikin shekaru 25 da suka gabata kacal, kamfanonin kasar Sin da suka zuba jari a nahiyar Afirka sun taimaka wa kasashen yankin da ginawa ko kara inganta sufurin jirgin kasa da ya kunshi layukan dogo fiye da kilomita 10,000, da manyan tituna da tsawonsu ya kai kusan kilomita 100,000, da gina manyan gadoji kimanin 1,000, baya ga tasoshin jiragen ruwa ciki har da masu zurfin ruwa da adadinsu ya kai 100, kana da habaka samar da wutar lantarki ta hanyar gina tasoshin janyowa da layukan rarrabawa da a kalla za su kai tsawon kilomita 66,000.

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Kasar Sin ta kuma himmatu wajen tallafa wa Afirka wajen gina masana’antu da za su rika sarrafa ko san’anta kayayyaki a cikin gida domin taimaka wa habakar tattalin arzikin yankin. Haka nan a bangaren ci gaban kimiyya da fasaha da aiki da sabbin makamashi marasa gurbata muhalli, kana bangaren aikin gona ma ba a bar shi a baya ba.

A tsakanin shekarun da ba su wuce 10 ba, kasar Sin ta gina cibiyoyin inganta fasahar aikin gona guda 24 a sassan Afirka tare da habaka fasahohin aikin gona daban-daban fiye da 300 wanda hakan ya taimaka gaya ga samun girbi mai albarka da a kalla kashi 30 zuwa 60 cikin dari inda manoma kimanin miliyan daya suka ci gajiyar abin.

Irin wannan zumunci ake so ya dawwama ana sadar da shi saboda kamar yadda Hausawa kan ce “na ji dadi shi ne batu, ba na saba ba!”(Abdulrazaq Yahuza Jere)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Bude Kasuwarta Ga Gyadar Sha Zawa Daga Nahiyar Afrika
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
  • Sulaiman
    Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Next Post
Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

Yawan Sakwannin Da Sin Ta Yi Jigila a Shekarar 2024 Ya Zarce Biliyan 170

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.