• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsananin Yunwa: Sarki Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashin Kayan Abinci A Yobe

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Dawanau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Damaturu, Alhaji Shehu Hashimi II, Ibn Umar Al-Amin Elkenemi, ya yi kira ga ‘yan kasuwa da ke Jihar Yobe su taimaka wa talakawa ta hanyar rage farashin kayayyakin abinci.

Sarkin ya nuna matukar damuwarsa kan yadda farashin kayayyakin masarufi suka yi tsada sosai wanda hakan ke gagaran talaka wajen ciyar da iyalansa.

  • An Aike Da Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi
  • Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

Da yake nuna rashin jin dadinsa kan yadda jama’a suke matukar shan wahala sakamakon fatara da yunwa a jihar, basaraken ya shaida wa LEADERSHIP a ranar Lahadi a masarautarsa da ke Damaturu cewa, “Akwai bukatar cikin gaggawa a yi kira ga ‘yan kasuwa da su saukaka farashin kayayyakin abinci ta yadda talakawa za su iya saya.”

Ya hori ‘yan kasuwan da su yi dukkanin mai yiyuwa wajen ganin sun zaftare farashin kayan abinci domin kishin al’umma da kuma taimaka wa masu karamin karfi da ke cikin al’umma.

A cewarsa, “Ina sanar da ku cewa, mun damu sosai kan hauhawar farashin kayayyakin abinci a jihar nan. Don haka ne nake jawo hankalin ‘yan kasuwa da su saukaka farashin kayan abinci ga jama’a, musamman talakawa da marasa karfi.”

Labarai Masu Nasaba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Ya lura kan cewa tsadar kayan bukatu, musamman kayan abinci, sun jefa jama’a cikin wahala da ukuba, don haka ne ma ya janyo hankalin gwamnati da ta ci gaba da taka nata rawar wajen taimaka wa jama’an da suke cikin talauci da marasa karfi.

Ya kuma nuna wahalhalun da ake ciki da matsin tattalin arziki da talakawa ke sha a matsayin abun damuwa ga kowa, musamman wadanda sai sun fita sun yi buga-bugar neman abun da za su sanya a bakin salati su da iyalansu a Jihar Yobe da ma Nijeriya baki daya.

Basaraken gargajiyan ya kara da ba da shawara ga ‘yan kasuwa da cewa su cire dukkanin wata kumbiya-kumbiya a cikin harkokin kasuwancinsu, domin ganin an tabbatar da cewa kayan abinci sun yi sauki ta yadda talaka zai iya saya.

Kazalika, ya nemi kungiyoyi da masu hannu da suni da su fito kwansu da kwarkwatarsu su taimaki mutanen da ke fama da bukata ta musamman wato nakasassu a cikin al’umma tare da marasa karfi a irin wannan mayuwacin halin matsin rayuwa da ake ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciTsadar RayuwaYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Cudanyar Al’adun Sin Da Tajikistan A Dushanbe

Next Post

An Wallafa Makalar Da Shugaba Xi Ya Rubuta A Tajikstan

Related

Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

39 minutes ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

2 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

2 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

6 hours ago
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai
Labarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

6 hours ago
Next Post
tajikstan

An Wallafa Makalar Da Shugaba Xi Ya Rubuta A Tajikstan

LABARAI MASU NASABA

Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.