• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsananin Yunwa: Sarki Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashin Kayan Abinci A Yobe

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
Dawanau

Sarkin Damaturu, Alhaji Shehu Hashimi II, Ibn Umar Al-Amin Elkenemi, ya yi kira ga ‘yan kasuwa da ke Jihar Yobe su taimaka wa talakawa ta hanyar rage farashin kayayyakin abinci.

Sarkin ya nuna matukar damuwarsa kan yadda farashin kayayyakin masarufi suka yi tsada sosai wanda hakan ke gagaran talaka wajen ciyar da iyalansa.

  • An Aike Da Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi
  • Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

Da yake nuna rashin jin dadinsa kan yadda jama’a suke matukar shan wahala sakamakon fatara da yunwa a jihar, basaraken ya shaida wa LEADERSHIP a ranar Lahadi a masarautarsa da ke Damaturu cewa, “Akwai bukatar cikin gaggawa a yi kira ga ‘yan kasuwa da su saukaka farashin kayayyakin abinci ta yadda talakawa za su iya saya.”

Ya hori ‘yan kasuwan da su yi dukkanin mai yiyuwa wajen ganin sun zaftare farashin kayan abinci domin kishin al’umma da kuma taimaka wa masu karamin karfi da ke cikin al’umma.

A cewarsa, “Ina sanar da ku cewa, mun damu sosai kan hauhawar farashin kayayyakin abinci a jihar nan. Don haka ne nake jawo hankalin ‘yan kasuwa da su saukaka farashin kayan abinci ga jama’a, musamman talakawa da marasa karfi.”

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

Ya lura kan cewa tsadar kayan bukatu, musamman kayan abinci, sun jefa jama’a cikin wahala da ukuba, don haka ne ma ya janyo hankalin gwamnati da ta ci gaba da taka nata rawar wajen taimaka wa jama’an da suke cikin talauci da marasa karfi.

Ya kuma nuna wahalhalun da ake ciki da matsin tattalin arziki da talakawa ke sha a matsayin abun damuwa ga kowa, musamman wadanda sai sun fita sun yi buga-bugar neman abun da za su sanya a bakin salati su da iyalansu a Jihar Yobe da ma Nijeriya baki daya.

Basaraken gargajiyan ya kara da ba da shawara ga ‘yan kasuwa da cewa su cire dukkanin wata kumbiya-kumbiya a cikin harkokin kasuwancinsu, domin ganin an tabbatar da cewa kayan abinci sun yi sauki ta yadda talaka zai iya saya.

Kazalika, ya nemi kungiyoyi da masu hannu da suni da su fito kwansu da kwarkwatarsu su taimaki mutanen da ke fama da bukata ta musamman wato nakasassu a cikin al’umma tare da marasa karfi a irin wannan mayuwacin halin matsin rayuwa da ake ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi
Labarai

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
Labarai

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Next Post
tajikstan

An Wallafa Makalar Da Shugaba Xi Ya Rubuta A Tajikstan

LABARAI MASU NASABA

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025
Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

Tawagar Likitocin Sin Ta Samar Da Tallafin Jinya Ga Kananan Yara Kyauta A Togo

October 19, 2025
Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.