• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsananin Yunwa: Sarki Ya Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Rage Farashin Kayan Abinci A Yobe

by Sulaiman and Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Dawanau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sarkin Damaturu, Alhaji Shehu Hashimi II, Ibn Umar Al-Amin Elkenemi, ya yi kira ga ‘yan kasuwa da ke Jihar Yobe su taimaka wa talakawa ta hanyar rage farashin kayayyakin abinci.

Sarkin ya nuna matukar damuwarsa kan yadda farashin kayayyakin masarufi suka yi tsada sosai wanda hakan ke gagaran talaka wajen ciyar da iyalansa.

  • An Aike Da Ɗan Shekara 67 Gidan Yari Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Mata 2 Fyaɗe Yana Ba Su ₦500 A Bauchi
  • Huldar Abotar Dindindin Tsakanin Sin Da Kazakhstan Na Samun Ci Gaba Zuwa Sabon Mataki

Da yake nuna rashin jin dadinsa kan yadda jama’a suke matukar shan wahala sakamakon fatara da yunwa a jihar, basaraken ya shaida wa LEADERSHIP a ranar Lahadi a masarautarsa da ke Damaturu cewa, “Akwai bukatar cikin gaggawa a yi kira ga ‘yan kasuwa da su saukaka farashin kayayyakin abinci ta yadda talakawa za su iya saya.”

Ya hori ‘yan kasuwan da su yi dukkanin mai yiyuwa wajen ganin sun zaftare farashin kayan abinci domin kishin al’umma da kuma taimaka wa masu karamin karfi da ke cikin al’umma.

A cewarsa, “Ina sanar da ku cewa, mun damu sosai kan hauhawar farashin kayayyakin abinci a jihar nan. Don haka ne nake jawo hankalin ‘yan kasuwa da su saukaka farashin kayan abinci ga jama’a, musamman talakawa da marasa karfi.”

Labarai Masu Nasaba

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Ya lura kan cewa tsadar kayan bukatu, musamman kayan abinci, sun jefa jama’a cikin wahala da ukuba, don haka ne ma ya janyo hankalin gwamnati da ta ci gaba da taka nata rawar wajen taimaka wa jama’an da suke cikin talauci da marasa karfi.

Ya kuma nuna wahalhalun da ake ciki da matsin tattalin arziki da talakawa ke sha a matsayin abun damuwa ga kowa, musamman wadanda sai sun fita sun yi buga-bugar neman abun da za su sanya a bakin salati su da iyalansu a Jihar Yobe da ma Nijeriya baki daya.

Basaraken gargajiyan ya kara da ba da shawara ga ‘yan kasuwa da cewa su cire dukkanin wata kumbiya-kumbiya a cikin harkokin kasuwancinsu, domin ganin an tabbatar da cewa kayan abinci sun yi sauki ta yadda talaka zai iya saya.

Kazalika, ya nemi kungiyoyi da masu hannu da suni da su fito kwansu da kwarkwatarsu su taimaki mutanen da ke fama da bukata ta musamman wato nakasassu a cikin al’umma tare da marasa karfi a irin wannan mayuwacin halin matsin rayuwa da ake ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbinciTsadar RayuwaYunwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Bikin Cudanyar Al’adun Sin Da Tajikistan A Dushanbe

Next Post

An Wallafa Makalar Da Shugaba Xi Ya Rubuta A Tajikstan

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

3 hours ago
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

4 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

17 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

18 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

20 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

23 hours ago
Next Post
tajikstan

An Wallafa Makalar Da Shugaba Xi Ya Rubuta A Tajikstan

LABARAI MASU NASABA

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.