ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
11 months ago
Kofin Duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da kasar Gabon a wasanta na gaba na neman tikitin zuwa gasar Kofin Duniya da za a buga a kasashen Amurka, Medico da Canada, wasan wanda za a buga a kasar Moroko ranar 13 ga watan Nuwamba zai zama sharar fage a wajen kasashen biyu, Nijeriya ta doke kasar Benin da ci 4-0 a wasan da suka buga a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom ranar Talata, wanda ya kasance wasa na karshe da kasar ta buga a cikin rukunin C inda ta kare a matsayi na biyu maki daya tsakaninta da Afirika Ta Kudu wadda ta kare a matsayi na 1.

 

Zakarun na Afrika har sau uku Nijeriya ta samu damar zuwa wasan Sili daya kwale bayan doke Jamhuriyar Benin, inda suka kare matsayi na biyu a rukuninsu na neman tikitin shiga gasar, ita kuma Gabon ta samu nasarar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasannin Play Off bayan nasarar da ta yi akan kasar Burundi da ci 2-0, nasarar da Ibory Coast ta samu a kan Kenya ne ya kara taimaka wa Gabon din kammala wasannin rukuni a matsayi na biyu a rukunin F.

ADVERTISEMENT
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
  • Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

A daya bangaren kuma DR Congo ta lallasa Sudan da ci 1-0, inda ta zo ta biyu a bayan Senegal a rukunin B, yayin da Kamaru ta kare a matsayi na biyu a rukunin D, kasashen Nijeriya, Gabon, DR Congo da Kamaru ne suka samu damar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasan Sili daya Kwale, domin samun wadda za ta kara da wata kasa a Nahiyar Turai wajen ganin sun samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

Za a gudanar da wasannin a kasar Morocco daga ranar 13 zuwa 16 ga watan Nuwamba, wanda zai kunshi Nijeriya da Gabon, sai kuma Kamaru da DR Congo, kasashen da suka yi nasara a wasan farko za su hadu da juna wasa na biyu domin fitar da zakara wanda zai buga wasa daya da wata kasa a Nahiyar Turai a watan Maris na shekarar 2026, dukkan wasannin za su kasance haduwa daya, sannan kuma za a iya karin mintuna 20 idan bukatar hakan ta taso (Edtra Time), ana sa ran hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF ta tabbatar da birane da wuraren da za su karbi bakuncin gasar a cikin kwanaki masu zuwa.

 

Yayin da kasashe 9 ne daga Afirika zuwa yanzu suka samu nasarar zuwa gasar Kofin Duniya, wasan na share fage na iya zama wata hanya da Afirika za ta samu karin wakilai daga Nahiyar wadanda za su samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya wadda kasashe 48 za su buga a shekarar 2026.

 

wasan na badi zai kasance Kofin Duniya na farko da kasashe fiye da 40 za su buga, kuma za a gudanar da shi a kasashe uku da suka hada da Amurka, Medico da Canada, a takaice Nijeriya na bukatar samun nasara a wasanni 3 da za ta buga a jere kafin samun damar zuwa gasar Kofin Duniya ta shekarar 2026.

Kofin Duniya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Yaushe Za A Fara Kofin Zakarun Turai
  • Abba Ibrahim Wada
    Messi Ya Yi Ritaya A Argentina: Da Me Za Mu Iya Tuna Gwarzon Duniyar?
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye ‘Yan wasan Nijeriya Da Za Su Buga Gasar Firimiyar Ingila Ta Bana?
  • Abba Ibrahim Wada
    Chelsea A Ƙarƙashin Xavi Alonso
Kofin Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana
Wasanni

Ƙungiyoyi 5 Da Ke Takarar Gwarzuwar Ƙungiya Ta Bana

September 8, 2026
Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain
Wasanni

Kofin Duniya: Yau Falconets Za Su Kece Raini Da Spain

September 7, 2026
Next Post
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga 'Yan Bindiga A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.