ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
8 months ago
Kofin Duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta kara da kasar Gabon a wasanta na gaba na neman tikitin zuwa gasar Kofin Duniya da za a buga a kasashen Amurka, Medico da Canada, wasan wanda za a buga a kasar Moroko ranar 13 ga watan Nuwamba zai zama sharar fage a wajen kasashen biyu, Nijeriya ta doke kasar Benin da ci 4-0 a wasan da suka buga a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom ranar Talata, wanda ya kasance wasa na karshe da kasar ta buga a cikin rukunin C inda ta kare a matsayi na biyu maki daya tsakaninta da Afirika Ta Kudu wadda ta kare a matsayi na 1.

 

Zakarun na Afrika har sau uku Nijeriya ta samu damar zuwa wasan Sili daya kwale bayan doke Jamhuriyar Benin, inda suka kare matsayi na biyu a rukuninsu na neman tikitin shiga gasar, ita kuma Gabon ta samu nasarar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasannin Play Off bayan nasarar da ta yi akan kasar Burundi da ci 2-0, nasarar da Ibory Coast ta samu a kan Kenya ne ya kara taimaka wa Gabon din kammala wasannin rukuni a matsayi na biyu a rukunin F.

ADVERTISEMENT
  • An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza
  • Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

A daya bangaren kuma DR Congo ta lallasa Sudan da ci 1-0, inda ta zo ta biyu a bayan Senegal a rukunin B, yayin da Kamaru ta kare a matsayi na biyu a rukunin D, kasashen Nijeriya, Gabon, DR Congo da Kamaru ne suka samu damar kasancewa cikin kasashen da za su buga wasan Sili daya Kwale, domin samun wadda za ta kara da wata kasa a Nahiyar Turai wajen ganin sun samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za a gudanar da wasannin a kasar Morocco daga ranar 13 zuwa 16 ga watan Nuwamba, wanda zai kunshi Nijeriya da Gabon, sai kuma Kamaru da DR Congo, kasashen da suka yi nasara a wasan farko za su hadu da juna wasa na biyu domin fitar da zakara wanda zai buga wasa daya da wata kasa a Nahiyar Turai a watan Maris na shekarar 2026, dukkan wasannin za su kasance haduwa daya, sannan kuma za a iya karin mintuna 20 idan bukatar hakan ta taso (Edtra Time), ana sa ran hukumar kwallon kafa ta Afirka CAF ta tabbatar da birane da wuraren da za su karbi bakuncin gasar a cikin kwanaki masu zuwa.

 

Yayin da kasashe 9 ne daga Afirika zuwa yanzu suka samu nasarar zuwa gasar Kofin Duniya, wasan na share fage na iya zama wata hanya da Afirika za ta samu karin wakilai daga Nahiyar wadanda za su samu tikitin zuwa gasar Kofin Duniya wadda kasashe 48 za su buga a shekarar 2026.

 

wasan na badi zai kasance Kofin Duniya na farko da kasashe fiye da 40 za su buga, kuma za a gudanar da shi a kasashe uku da suka hada da Amurka, Medico da Canada, a takaice Nijeriya na bukatar samun nasara a wasanni 3 da za ta buga a jere kafin samun damar zuwa gasar Kofin Duniya ta shekarar 2026.

Kofin Duniya
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?
Kofin Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga 'Yan Bindiga A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.