• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (TUC), wacce hadakar manyan kungiyoyin ma’aikata daban-daban ce a Nijeriya, ta bai wa Gwamnonin Jihar Gombe da na Bauchi, Muhammadu Inuwa Yahaya da Bala Muhammad lambobin yabo ta ‘Gwamnoni Masu Kaunar Ma’aikata’ bisa la’akari da kyawawan manufofi da jajircewar su na inganta aikin gwamnati.

An bai wa Gwamnonin lambar yabon ce yayin wata liyafar cin abincin dare da kungiyar ta TUC ta kasa ta shirya a babban dakin taro na kasa da kasa dake Abuja kwanaki kamar yadda hadiman Gwamnonin, Kwamared Mukhtar M. Gidado, da Alhaji Ismaila Uba Misilli na gwamnan Bauchi da Gombe bi da bi suka fitar a wata sanarwa daban-daban.

  • Rasha Ta Zargi Ukraine Da Yunkurin Kashe Putin A Harin Jiragen Yaki Marasa Matuki A Kremlin

A cewar shugaban kungiyar ta TUC na kasa, Kwamared Festus Osifo, an karrama Gwamna Inuwan ne duba da yadda gwamnatinsa take gaggawar biyan albashin ma’aikata da fansho tare da biyan basussukan kudaden giratuti da gwamnatocin baya suka ki biya a jihar, da kuma sauran manufofin dake daɗaɗawa ma’aikata.

Haka zancen yake ga gwamnan Bauchi, inda kungiyar ta ce, tun hawan kujerar gwamnan Bala Mohammed ya shagaltu domin lalibo bakin zaren magance matsalolin da ma’aikata ke fuskata tare da saukaka musu yanayin aiki mai inganci, biyan albashi a kan kari da rage basuka giratuti da fansho da tsoffin ma’aikata ke bi.

Bauchi

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

A yayin bikin, Gwamna Inuwa ya samu wakilcin mataimakin sa ne Dr Mannasah Daniel Jatau, yayin da shi Kuma na jihar Bauchi, ya samu wakilcin Muhammad Auwal Jatau, mataimakin gwamnan Jihar (zababbe) inda suka amshi lambar yabon a madadin Gwamnonin.

Da ya ke jawabi a madadin gwamnan Gonbe, Dr. Manassah Jatau ya gode wa shugabannin kungiyar ta TUC bisa karramawar, wacce ya bayyana a matsayin kalubale na ƙara jajircewa.

Ya ce, “Bai wa mutum lambar yabo tamkar an kalubalance shi ne; don haka duk wadanda aka bai wa lambar yabo a yau, to fa an kalubalance su ne su kara kokari. Mun karbi wannan kalubalen da hannu bibbiyu don cika muradun kungiyar TUC da ma na ma’aikata baki daya”.

Shi ma Jatau ya ce, lambar yabon da aka bai wa gwamna Bala Muhammad ba ta zo musu da mamaki ba domin yadda suka ga gwamnan ya tashi tsaye wajen sauke nauyin da ke kansa da kyautata rayuwar al’umma, hade da zama gwamnan da ke kaunar cigaban aiki a kowani lokaci.

Wakilan Gwamnonin suka ce: “Kofofin mu za su ci gaba da kasancewa a bude ga kungiyar TUC, kuma za mu ci gaba da bada goyon bayan mu a kodayaushe ga TUC da ma’aikata don samar musu kyakkywan yanayin aiki don gudanar da ayyukan su cikin lumana da kwanciyar hankali”.

“Gwamnatocinmu ta ma’aikata ce. A kullum muna bai wa jin dadi da walwalan ma’aikatan jihohinmu muhimmanci a manufofin mu na ci gaba, ciki har da sake fasali da farfado da tsarin aikin gwamnati, da biyan albashi da fansho akan kari, dana biyan bashin kudaden fansho da na sallaman ma’aikata wato giratuti wadda gwamnatocin baya suka gaza biya kamar dai yadda shugabannin kungiyar ta TUC suka bada shaida”.

Bauchi

Taron ya samu halartar sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha, da gwamnonin jihohin Edo da Bauchi, da Rivers da kuma Nasarawa wadanda suka samu wakilci, da Manajan Daraktan Kamfanin Mai na Kasa NNPC Limited Mele Kolo Kyari, da Sarkin Dass da shugabannin kungiyoyin ƙwadago da jami’an diflomasiyya da shugabannin kamfanoni da dai sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Bukaci Kungiyar WTO Da Ta Kara Sanya Ido Kan Karan Tsaye Ga Ka’idojin Da Amurka Ta Yi

Next Post

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Related

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

34 minutes ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

3 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

4 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba
Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

5 hours ago
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa
Manyan Labarai

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

6 hours ago
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22
Labarai

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

7 hours ago
Next Post
Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Rukunin Farko Na 'Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

Bello Yabo Ya Je Wajen Wa’azi Da Bindiga A Sakkwato, Ya Ce Ya Shirya Kare Kansa

June 3, 2025
FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

FRSC Ta Fara Binciken Hatsarin Motar Da Ya Yi Ajalin ’Yan Wasan Kano 22

June 3, 2025
FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

FERMA Na Bukatar N880bn Duk Shekara Domin Gyaran Tituna – Minista

June 3, 2025
Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

Kasar Sin: Amurka Ta Yi Matukar Kawo Cikas Ga Yarjejeniyar Da Aka Cimma A Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.