• English
  • Business News
Saturday, May 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (TUC), wacce hadakar manyan kungiyoyin ma’aikata daban-daban ce a Nijeriya, ta bai wa Gwamnonin Jihar Gombe da na Bauchi, Muhammadu Inuwa Yahaya da Bala Muhammad lambobin yabo ta ‘Gwamnoni Masu Kaunar Ma’aikata’ bisa la’akari da kyawawan manufofi da jajircewar su na inganta aikin gwamnati.

An bai wa Gwamnonin lambar yabon ce yayin wata liyafar cin abincin dare da kungiyar ta TUC ta kasa ta shirya a babban dakin taro na kasa da kasa dake Abuja kwanaki kamar yadda hadiman Gwamnonin, Kwamared Mukhtar M. Gidado, da Alhaji Ismaila Uba Misilli na gwamnan Bauchi da Gombe bi da bi suka fitar a wata sanarwa daban-daban.

  • Rasha Ta Zargi Ukraine Da Yunkurin Kashe Putin A Harin Jiragen Yaki Marasa Matuki A Kremlin

A cewar shugaban kungiyar ta TUC na kasa, Kwamared Festus Osifo, an karrama Gwamna Inuwan ne duba da yadda gwamnatinsa take gaggawar biyan albashin ma’aikata da fansho tare da biyan basussukan kudaden giratuti da gwamnatocin baya suka ki biya a jihar, da kuma sauran manufofin dake daɗaɗawa ma’aikata.

Haka zancen yake ga gwamnan Bauchi, inda kungiyar ta ce, tun hawan kujerar gwamnan Bala Mohammed ya shagaltu domin lalibo bakin zaren magance matsalolin da ma’aikata ke fuskata tare da saukaka musu yanayin aiki mai inganci, biyan albashi a kan kari da rage basuka giratuti da fansho da tsoffin ma’aikata ke bi.

Bauchi

Labarai Masu Nasaba

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

A yayin bikin, Gwamna Inuwa ya samu wakilcin mataimakin sa ne Dr Mannasah Daniel Jatau, yayin da shi Kuma na jihar Bauchi, ya samu wakilcin Muhammad Auwal Jatau, mataimakin gwamnan Jihar (zababbe) inda suka amshi lambar yabon a madadin Gwamnonin.

Da ya ke jawabi a madadin gwamnan Gonbe, Dr. Manassah Jatau ya gode wa shugabannin kungiyar ta TUC bisa karramawar, wacce ya bayyana a matsayin kalubale na ƙara jajircewa.

Ya ce, “Bai wa mutum lambar yabo tamkar an kalubalance shi ne; don haka duk wadanda aka bai wa lambar yabo a yau, to fa an kalubalance su ne su kara kokari. Mun karbi wannan kalubalen da hannu bibbiyu don cika muradun kungiyar TUC da ma na ma’aikata baki daya”.

Shi ma Jatau ya ce, lambar yabon da aka bai wa gwamna Bala Muhammad ba ta zo musu da mamaki ba domin yadda suka ga gwamnan ya tashi tsaye wajen sauke nauyin da ke kansa da kyautata rayuwar al’umma, hade da zama gwamnan da ke kaunar cigaban aiki a kowani lokaci.

Wakilan Gwamnonin suka ce: “Kofofin mu za su ci gaba da kasancewa a bude ga kungiyar TUC, kuma za mu ci gaba da bada goyon bayan mu a kodayaushe ga TUC da ma’aikata don samar musu kyakkywan yanayin aiki don gudanar da ayyukan su cikin lumana da kwanciyar hankali”.

“Gwamnatocinmu ta ma’aikata ce. A kullum muna bai wa jin dadi da walwalan ma’aikatan jihohinmu muhimmanci a manufofin mu na ci gaba, ciki har da sake fasali da farfado da tsarin aikin gwamnati, da biyan albashi da fansho akan kari, dana biyan bashin kudaden fansho da na sallaman ma’aikata wato giratuti wadda gwamnatocin baya suka gaza biya kamar dai yadda shugabannin kungiyar ta TUC suka bada shaida”.

Bauchi

Taron ya samu halartar sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha, da gwamnonin jihohin Edo da Bauchi, da Rivers da kuma Nasarawa wadanda suka samu wakilci, da Manajan Daraktan Kamfanin Mai na Kasa NNPC Limited Mele Kolo Kyari, da Sarkin Dass da shugabannin kungiyoyin ƙwadago da jami’an diflomasiyya da shugabannin kamfanoni da dai sauran su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Bukaci Kungiyar WTO Da Ta Kara Sanya Ido Kan Karan Tsaye Ga Ka’idojin Da Amurka Ta Yi

Next Post

Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Related

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

12 hours ago
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci
Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

14 hours ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

15 hours ago
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
Labarai

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

16 hours ago
GORON JUMA’A 09/05/2025
Labarai

GORON JUMA’A 09/05/2025

17 hours ago
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 
Labarai

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

18 hours ago
Next Post
Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Rukunin Farko Na 'Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

Likitocin Sin Sun Ba Da Jinya Kyauta A Yankunan Karkara Na Saliyo

May 9, 2025
Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

Babban Bankin Sin Zai Inganta Hidimomin Kudi Don Habaka Amfani Da Shi

May 9, 2025
Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani

May 9, 2025
Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha

May 9, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.