ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsare-Tsare Ga Ma’aikata: Gwamnonin Bauchi Da Gombe Sun Samu Babbar Lambar Yabo Daga Kungiyar Kwadago Ta TUC

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (TUC), wacce hadakar manyan kungiyoyin ma’aikata daban-daban ce a Nijeriya, ta bai wa Gwamnonin Jihar Gombe da na Bauchi, Muhammadu Inuwa Yahaya da Bala Muhammad lambobin yabo ta ‘Gwamnoni Masu Kaunar Ma’aikata’ bisa la’akari da kyawawan manufofi da jajircewar su na inganta aikin gwamnati.

An bai wa Gwamnonin lambar yabon ce yayin wata liyafar cin abincin dare da kungiyar ta TUC ta kasa ta shirya a babban dakin taro na kasa da kasa dake Abuja kwanaki kamar yadda hadiman Gwamnonin, Kwamared Mukhtar M. Gidado, da Alhaji Ismaila Uba Misilli na gwamnan Bauchi da Gombe bi da bi suka fitar a wata sanarwa daban-daban.

  • Rasha Ta Zargi Ukraine Da Yunkurin Kashe Putin A Harin Jiragen Yaki Marasa Matuki A Kremlin

A cewar shugaban kungiyar ta TUC na kasa, Kwamared Festus Osifo, an karrama Gwamna Inuwan ne duba da yadda gwamnatinsa take gaggawar biyan albashin ma’aikata da fansho tare da biyan basussukan kudaden giratuti da gwamnatocin baya suka ki biya a jihar, da kuma sauran manufofin dake daɗaɗawa ma’aikata.

ADVERTISEMENT

Haka zancen yake ga gwamnan Bauchi, inda kungiyar ta ce, tun hawan kujerar gwamnan Bala Mohammed ya shagaltu domin lalibo bakin zaren magance matsalolin da ma’aikata ke fuskata tare da saukaka musu yanayin aiki mai inganci, biyan albashi a kan kari da rage basuka giratuti da fansho da tsoffin ma’aikata ke bi.

Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

A yayin bikin, Gwamna Inuwa ya samu wakilcin mataimakin sa ne Dr Mannasah Daniel Jatau, yayin da shi Kuma na jihar Bauchi, ya samu wakilcin Muhammad Auwal Jatau, mataimakin gwamnan Jihar (zababbe) inda suka amshi lambar yabon a madadin Gwamnonin.

Da ya ke jawabi a madadin gwamnan Gonbe, Dr. Manassah Jatau ya gode wa shugabannin kungiyar ta TUC bisa karramawar, wacce ya bayyana a matsayin kalubale na ƙara jajircewa.

Ya ce, “Bai wa mutum lambar yabo tamkar an kalubalance shi ne; don haka duk wadanda aka bai wa lambar yabo a yau, to fa an kalubalance su ne su kara kokari. Mun karbi wannan kalubalen da hannu bibbiyu don cika muradun kungiyar TUC da ma na ma’aikata baki daya”.

Shi ma Jatau ya ce, lambar yabon da aka bai wa gwamna Bala Muhammad ba ta zo musu da mamaki ba domin yadda suka ga gwamnan ya tashi tsaye wajen sauke nauyin da ke kansa da kyautata rayuwar al’umma, hade da zama gwamnan da ke kaunar cigaban aiki a kowani lokaci.

Wakilan Gwamnonin suka ce: “Kofofin mu za su ci gaba da kasancewa a bude ga kungiyar TUC, kuma za mu ci gaba da bada goyon bayan mu a kodayaushe ga TUC da ma’aikata don samar musu kyakkywan yanayin aiki don gudanar da ayyukan su cikin lumana da kwanciyar hankali”.

“Gwamnatocinmu ta ma’aikata ce. A kullum muna bai wa jin dadi da walwalan ma’aikatan jihohinmu muhimmanci a manufofin mu na ci gaba, ciki har da sake fasali da farfado da tsarin aikin gwamnati, da biyan albashi da fansho akan kari, dana biyan bashin kudaden fansho da na sallaman ma’aikata wato giratuti wadda gwamnatocin baya suka gaza biya kamar dai yadda shugabannin kungiyar ta TUC suka bada shaida”.

Bauchi

Taron ya samu halartar sakataren gwamnatin tarayya Boss Mustapha, da gwamnonin jihohin Edo da Bauchi, da Rivers da kuma Nasarawa wadanda suka samu wakilci, da Manajan Daraktan Kamfanin Mai na Kasa NNPC Limited Mele Kolo Kyari, da Sarkin Dass da shugabannin kungiyoyin ƙwadago da jami’an diflomasiyya da shugabannin kamfanoni da dai sauran su.

Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Rukunin Farko Na ‘Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

Rukunin Farko Na 'Yan Nijeriya 376 Da Aka Kwaso A Sudan Sun Iso Abuja

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.