• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Zai Ba Kasashe Masu Tasowa Damar Tabbatar Da Makoma Mai Haske

by CMG Hausa
2 years ago
BRICS

A kwanakin nan, wasu kafofin watsa labaru sun gabatar da labarin cewa, Anil Sooklal, manzon kasar Afirka ta Kudu mai kula da aikin tsarin kasashen BRICS, ya ce wasu kasashe 25 zuwa 30 sun riga sun gabatar da bukatar zama mambobin tsarin BRICS, ciki har da Najeriya, da Masar, da Habasha, da Zimbabwe, da Aljeriya, da Tunisia, da Sudan, da suka kasance a nahiyar Afirka, gami da sauran kasashe masu tasowa na Latin Amurka, da Gabas ta Tsakiya, da na gabashin Turai. 

To ko mene ne dalilin da ya sa tsarin BRICS da kasashen Sin, da Afirka ta Kudu, da India, da Brazil, da Rasha suka kafa ke janyo hankalin dimbin kasashe masu tasowa?

  • Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

A gani na, kalmomin shugaba Bola Tinubu na kasar Najeriya, cikin jawabin da ya gabatar a gun wani taro na kungiyar tarayyar Afirka ta AU a kwanan baya, sun nuna dalilin da muke nema. A cewar shugaban, “Abubuwan da suka faru a shekarun nan sun nuna mana cewa, tattalin arzikin duniya zai iya gamuwa da matsalar tsaiko da yanayi na koma baya. Idan mu kasashen Afirka ba mu yi kokarin daukar matakai don tinkarar matsalolin da aka samu ba, to, za mu iya fadawa cikin mawuyacin hali.” Ma’anar maganarsa ita ce, ya kamata kasashen Afirka da kasashe masu tasowa na sauran yankuna su dauki kwararan matakai, a kokarin tinkarar kalubaloli, da koma bayan tattalin arzikin duniya ya janyo, don tabbatar da makomarsu mai haske a nan gaba. Sai dai ba za a cimma wannan buri ba, ba tare da hadin gwiwar kasashe masu tasowa ba.

Tsarin hadin gwiwar kasashen BRICS ya kunshi manyan kasashe masu tasowa 5 yanzu. Alkaluman shekarar 2021 sun nuna cewa, darajar tattalin arzikin kasashen BRICS ta kai kashi 25.24% na darajar tattalin arzikin daukacin kasashen duniya, adadin da har ya zarce darajar tattalin arziki na kungiyar G7, dake karkashin jagorancin kasar Amurka. Saboda haka, tsarin BRICS ya zama wani muhimmin dandalin dake baiwa kasashe masu tasowa damar bayyana bukatunsu na bai daya, da samar da karin tasiri a duniya, don kare moriyarsu ta bai daya, ta yadda kasashen za su zama masu fada-a-ji a duniya, da cimma burinsu na samar da wani tsarin kasa da kasa mai daidaito dake haifar da alfanu ga daukacin dan Adam.

Sa’an nan idan mun yi nazari kan amfanin tsarin BRICS a bangarori daban daban, to, da farko, a fannin tsaron hada-hadar kudi, tsarin ya samar da damar yin amfani da nau’ikan kudi daban daban a fannin cinikin kasa da kasa. Mun san kasashen duniya suna shan wahalar babakeren da kasar Amurka ke yi bisa matsayin kudin dala na kasar, a matsayin sa na kudin da ake yin amfani da shi wajen cinikin kasa da kasa mafi muhimmanci a duniya. Inda karuwar ruwan bashi a kasar Amurka, da hauhawar darajar dalar Amurka, wasu manyan dalilai ne da suka haddasa hauhawar farashin kayayyaki, da karuwar bashin da ake binsu, a dimbin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen dake nahiyar Afirka da yawa. Saboda haka, kasashen BRICS sun mai da “samar da sabon kudin da za a iya yin amfani da shi wajen yin cinikin kasa da kasa” batu na farko da za su tattauna a kai wajen taron kolin su da zai gudana a watan Agusta mai zuwa. Tattalin arizki mai karfi na kasashen BRICS, ya samar da damar daidaita wannan batu, abun da ya faranta ran dimbin kasashe masu tasowa.

LABARAI MASU NASABA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Ban da haka, a fannin aikin siyasa da ya shafi bangarori daban daban, kasashe masu tasowa na fatan yin amfani da tsarin BRICS wajen samun daidaito a duniya, da wakiltar moriyarsu ta bai daya, maimakon zama karkashin tilastawar da kasashen yamma ke yi musu. Misali, game da yakin da ake yi tsakanin kasashen Ukraine da Rasha, kasashen yamma na neman kara tayar da wutar yaki, kuma ba su son ganin tsagaita bude wuta, yayin da kasashen Afirka da kasar Sin suke daukar matsayi na ’yan ba ruwanmu, da kokarin yin sulhu. Wannan bambancin ra’ayi ya nuna cewa, dole ne a samu mabambantan bangarori masu tunani da moriya daban daban a harkar siyasar kasa da kasa.

Kana a fannin tattalin arziki, bisa la’akari da yanayin tattalin arziki mai wuya da duniyarmu ke ciki, kasashen yamma na dauke da tunani na son kai, wanda ya saba da ka’idar kasa da kasa ta samun yanayin zaman daidai wa daida, da yin ciniki cikin ’yanci. Inda suke neman hana sauran kasashe samun ci gaban tattalin arziki, da sanya kasashe masu tasowa shan karin wahalhalu na koma bayan tattalin arziki, ta yadda su kansu za su samu sauki. Wannan sam ba wani abu ba ne da kasashe masu tasowa ke son gani ba. Saboda haka suna kokarin karfafa hadin gwiwa tare da kasashen BRICS, gami da neman wakilcinsu a tsarin BRICS, don samar da damammakin biyan bukatunsu na neman samun ci gaba.

Hakika a lokacin da kafofin watsa labaru na kasashen yamma suka mai da hankali kan ko shugaban kasar Rasha Vladimir Putin, wanda ke da “laifin ta da yaki” a ganinsu, zai tafi kasar Afirka ta Kudu don halartar taron koli na tsarin kasashen BRICS, kasashe masu tasowa da yawa na kokarin neman halartar tsarin BRICS.

Wannan mataki ya nuna bambancin tunanin kasashen yamma da na kasashe masu tasowa, wato kasashen yamma na mai da hankali kan arangamar da ake yi yanzu, yayin da kasashe masu tasowa ke dora muhimmanci kan neman ci gaba, da tabbatar da makoma mai haske. Sannu a hankali, wannan bambancin tunani zai iya haifar da babban sauyi a yanayin tsare-tsaren duniyar mu. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai
Daga Birnin Sin

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya
Daga Birnin Sin

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%
Daga Birnin Sin

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Next Post
Sabuwar Shekarar Musulunci: Jihar Kano Ta Ba Da Hutun Gobe Laraba

Sabuwar Shekarar Musulunci: Jihar Kano Ta Ba Da Hutun Gobe Laraba

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba

Ba Za A Samu Ƙarancin Man Fetur A Lokutan Bukukuwan Ƙarshen Shekara Ba – Dangote 

October 27, 2025
An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

An Zaɓi Birgediya Janar Yake A Matsayin Sarkin Sayawa Na Farko Duk Da Zanga-zanga 

October 27, 2025
BRICS

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.