• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Zai Samar Da Yanayi Na Daidaito Ga Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsarin BRICS Zai Samar Da Yanayi Na Daidaito Ga Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Za a gudanar da taron shugabannin kasashen BRICS (Brazil, Rasha, India, Sin, da Afirka ta Kudu) karo na 15 tsakanin ranar 22 zuwa ta 24 ga wata, a kasar Afirka ta Kudu, wanda ya fi jawo hankalin al’umma ta fannoni biyu:

Na farko, za a tattauna wasu abubuwa masu muhimmanci wajen taron, da suka hada da yadda za a rage dogaro kan dalar Amurka a matsayin kudin musayar da ake yawan yin amfani da shi yayin cinikin kasa da kasa, da habakar tsarin hadin gwiwar kasashen BRICS don ya kunshi karin kasashe.

Na biyu shi ne yadda taron da tsarin BRICS ke samun karbuwa tsakanin kasashe masu tasowa. A cewar kasar Afirka ta kudu, wadda za ta karbi kabunkin taron kolin BRICS na wannan karo, a kalla shugabannin kasashe masu tasowa 34 sun tabbatar da cewa za su halarci tarukan shawarwari da za a gudanar da su a gefen taron. Kana wasu kasashe masu tasowa a kalla 23, da suka hada da Najeriya, da Masar, da Iran, da dai sauransu, sun riga sun bayyana niyyar neman zama mambobin tsarin BRICS.

To, ko me ya sa dimbin kasashe masu tasowa ke sha’awar tsarin hadin gwiwa na BRICS?
Dalili na farko shi ne, a ganin kasashe masu tasowa, tsarin nan zai taimakawa biyan bukatunsu a fannin raya kasa, wadanda suka hada da rage ko kuma daina dogaro kan dalar Amurka, don tabbatar da tsaronsu a fannonin hada-hadar kudi da tattalin arziki, da janyo karin jari daga ketare, da habaka huldar ciniki tsakanin kasashe masu tasowa, gami da kara zama masu fada a ji a duniya, da dai sauransu.

Ban da haka, wani dalili na daban, wanda ya fi muhimmanci, shi ne burin kasashe masu tasowa na neman sauya halin da suke ciki. A yayin da ake fama da tabarbarewar tattalin arzikin duniya, da yakin da aka dade ana gudanarwa tsakanin Rasha da Ukraine, tsohon tsarin hada-hadar kudi da na tattalin arzikin duniya, karkashin jagorancin kasashen yamma, sun riga sun zama tsare-tsaren da kasashe masu sukuni ke yin amfani da su wajen kare moriyarsu, maimakon samar da damar samun ci gaban tattalin arziki ga kasashe masu tasowa. Saboda haka, su kasashe masu tasowa ba yadda za su yi, ban da kokarin yin amfani da tsare-tsaren hadin gwiwa, da suka hada da tsarin BRICS, wajen tabbatar da wani yanayi na daidaito a fannin tsare-tsaren hada-hadar kudi da tattalin arziki, da samar da sabbin damamaki na raya kasa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A nasu bangare, wasu jami’an kungiyoyin kasa da kasa da masana na kasashen Afirka sun yaba da tsarin BRICS, da bayyana kakkyawan fata dangane da taron kolin dake tafe. Yayin da yake hira da manema labaru a kwanan baya, Carlos Correa, darektan zartaswa na kungiyar kasa da kasa ta raya kasashe masu tasowa ta South Centre, ya ce, kungiyoyin G7 da G20 suna karkashin kulawar kasashe masu sukuni, yayin da tsarin BRICS ke samar da manufofin da za su amfani kasashe masu tasowa. A nashi bangare, Fulufhelo Netswera, darektan cibiyar nazarin kasashen BRICS ta jami’ar Durban University of Tecnology ta kasar Afirka ta Kudu, ya yi hasashen cewa za a tattauna batun yin gyare-gyare kan tsarin MDD da na wasu kungiyoyin kasa da kasa yayin taron kolin BRICS dake tafe.

A ganinsa, tsarin duniya da aka kafa bayan yakin duniya na biyu ya ba da damamakin ci da gumin jama’ar kasashe masu raunin karfin tattalin arziki, saboda haka ana bukatar gyare-gyare don neman baiwa dukkan kasashe damar bayyana ra’ayoyinsu dangane da harkokin kasa da kasa.

Ban da haka, Charles Onunaiju, wani masani dan kasar Najeriya, ya ce, kasashen BRICS tamkar mambobin iyali ne da suke kokarin rufa wa juna baya, da hadin kai don tabbatar da moriyar junansu, don haka shigar kasashen Afirka cikin tsarin BRICS zai ba su damar daidaita matsalolin da suke hana ci gaban tattalin arzikinsu.

Wani abu mai ban sha’awa shi ne, ganin yadda tsarin BRICS ke jan hankalin kasashen Afirka ya sa kasashen yamma fara tunani kan laifinsu. A kwanan baya, majalisa mai kula da hulda da kasashen ketare ta kasar Amurka (Council on Foreign Relations) ta watsa wani bayani kan shafin yanar gizo nata, mai taken “Darasin da ya kamata a koya daga manufofin kasashen Afirka cikin sabon zamani”, wanda ya ce “Mutanen kasashen Afirka sun ki yin amfani da tsoffin dabaru wajen daidaita sabbin matsaloli”, saboda “ tsare-tsaren duniya na yanzu ya bakanta musu rai”.

“ Ya kamata Washington ta samu damar shaida cewa ita ma tana so ta shiga yunkurin garambawul kan tsare-tsaren duniya, saboda ba a yi la’akari da bukatar tabbatarwa kasashen Afirka da wani yanayi mai daidaito ba, a lokacin da aka gabatar da tsare-tsaren.” in ji bayanin.

Hakika fasahohin da kasar Sin ta samu ta hanyar raya kanta sun riga sun nuna cewa, samar da yanayi mai daidaito, da damar samun wadatar bai daya, tushe ne ga yunkurin samun ci gaban zaman al’umma mai inganci da dorewa.

Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin jaddada muhimmancin raya huldar abota dake iya samar da wani yanayi na daidaito tare da sauran kasashe, da kokarin kawar da gibin da ake samu tsakanin mabambantan kasashe ta fuskar ci gaban tattalin arizki, a cikin shawarar da kasar ta gabatar ta “kokarin tabbatar da ci gaban duniya”.

Abun da kasar Sin ke nema shi ma buri na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa. Za mu iya tabbatar da cewa, za a yi kokarin kula da wannan buri, da neman cika shi, a taron kolin tsarin BRICS na wannan karo. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sai Da Ruwan Ciki…

Next Post

‘Yan Bindiga Na Shirin Sake Kai Wa Jirgin Abuja Zuwa Kaduna Hari – DSS Ta Yi Gargadi

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

7 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

8 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

10 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

13 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

14 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

15 hours ago
Next Post
‘Yan Bindiga Na Shirin Sake Kai Wa Jirgin Abuja Zuwa Kaduna Hari – DSS Ta Yi Gargadi

'Yan Bindiga Na Shirin Sake Kai Wa Jirgin Abuja Zuwa Kaduna Hari - DSS Ta Yi Gargadi

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.