ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Zai Samar Da Yanayi Na Daidaito Ga Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

Za a gudanar da taron shugabannin kasashen BRICS (Brazil, Rasha, India, Sin, da Afirka ta Kudu) karo na 15 tsakanin ranar 22 zuwa ta 24 ga wata, a kasar Afirka ta Kudu, wanda ya fi jawo hankalin al’umma ta fannoni biyu:

Na farko, za a tattauna wasu abubuwa masu muhimmanci wajen taron, da suka hada da yadda za a rage dogaro kan dalar Amurka a matsayin kudin musayar da ake yawan yin amfani da shi yayin cinikin kasa da kasa, da habakar tsarin hadin gwiwar kasashen BRICS don ya kunshi karin kasashe.

Na biyu shi ne yadda taron da tsarin BRICS ke samun karbuwa tsakanin kasashe masu tasowa. A cewar kasar Afirka ta kudu, wadda za ta karbi kabunkin taron kolin BRICS na wannan karo, a kalla shugabannin kasashe masu tasowa 34 sun tabbatar da cewa za su halarci tarukan shawarwari da za a gudanar da su a gefen taron. Kana wasu kasashe masu tasowa a kalla 23, da suka hada da Najeriya, da Masar, da Iran, da dai sauransu, sun riga sun bayyana niyyar neman zama mambobin tsarin BRICS.

ADVERTISEMENT

To, ko me ya sa dimbin kasashe masu tasowa ke sha’awar tsarin hadin gwiwa na BRICS?
Dalili na farko shi ne, a ganin kasashe masu tasowa, tsarin nan zai taimakawa biyan bukatunsu a fannin raya kasa, wadanda suka hada da rage ko kuma daina dogaro kan dalar Amurka, don tabbatar da tsaronsu a fannonin hada-hadar kudi da tattalin arziki, da janyo karin jari daga ketare, da habaka huldar ciniki tsakanin kasashe masu tasowa, gami da kara zama masu fada a ji a duniya, da dai sauransu.

Ban da haka, wani dalili na daban, wanda ya fi muhimmanci, shi ne burin kasashe masu tasowa na neman sauya halin da suke ciki. A yayin da ake fama da tabarbarewar tattalin arzikin duniya, da yakin da aka dade ana gudanarwa tsakanin Rasha da Ukraine, tsohon tsarin hada-hadar kudi da na tattalin arzikin duniya, karkashin jagorancin kasashen yamma, sun riga sun zama tsare-tsaren da kasashe masu sukuni ke yin amfani da su wajen kare moriyarsu, maimakon samar da damar samun ci gaban tattalin arziki ga kasashe masu tasowa. Saboda haka, su kasashe masu tasowa ba yadda za su yi, ban da kokarin yin amfani da tsare-tsaren hadin gwiwa, da suka hada da tsarin BRICS, wajen tabbatar da wani yanayi na daidaito a fannin tsare-tsaren hada-hadar kudi da tattalin arziki, da samar da sabbin damamaki na raya kasa.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

A nasu bangare, wasu jami’an kungiyoyin kasa da kasa da masana na kasashen Afirka sun yaba da tsarin BRICS, da bayyana kakkyawan fata dangane da taron kolin dake tafe. Yayin da yake hira da manema labaru a kwanan baya, Carlos Correa, darektan zartaswa na kungiyar kasa da kasa ta raya kasashe masu tasowa ta South Centre, ya ce, kungiyoyin G7 da G20 suna karkashin kulawar kasashe masu sukuni, yayin da tsarin BRICS ke samar da manufofin da za su amfani kasashe masu tasowa. A nashi bangare, Fulufhelo Netswera, darektan cibiyar nazarin kasashen BRICS ta jami’ar Durban University of Tecnology ta kasar Afirka ta Kudu, ya yi hasashen cewa za a tattauna batun yin gyare-gyare kan tsarin MDD da na wasu kungiyoyin kasa da kasa yayin taron kolin BRICS dake tafe.

A ganinsa, tsarin duniya da aka kafa bayan yakin duniya na biyu ya ba da damamakin ci da gumin jama’ar kasashe masu raunin karfin tattalin arziki, saboda haka ana bukatar gyare-gyare don neman baiwa dukkan kasashe damar bayyana ra’ayoyinsu dangane da harkokin kasa da kasa.

Ban da haka, Charles Onunaiju, wani masani dan kasar Najeriya, ya ce, kasashen BRICS tamkar mambobin iyali ne da suke kokarin rufa wa juna baya, da hadin kai don tabbatar da moriyar junansu, don haka shigar kasashen Afirka cikin tsarin BRICS zai ba su damar daidaita matsalolin da suke hana ci gaban tattalin arzikinsu.

Wani abu mai ban sha’awa shi ne, ganin yadda tsarin BRICS ke jan hankalin kasashen Afirka ya sa kasashen yamma fara tunani kan laifinsu. A kwanan baya, majalisa mai kula da hulda da kasashen ketare ta kasar Amurka (Council on Foreign Relations) ta watsa wani bayani kan shafin yanar gizo nata, mai taken “Darasin da ya kamata a koya daga manufofin kasashen Afirka cikin sabon zamani”, wanda ya ce “Mutanen kasashen Afirka sun ki yin amfani da tsoffin dabaru wajen daidaita sabbin matsaloli”, saboda “ tsare-tsaren duniya na yanzu ya bakanta musu rai”.

“ Ya kamata Washington ta samu damar shaida cewa ita ma tana so ta shiga yunkurin garambawul kan tsare-tsaren duniya, saboda ba a yi la’akari da bukatar tabbatarwa kasashen Afirka da wani yanayi mai daidaito ba, a lokacin da aka gabatar da tsare-tsaren.” in ji bayanin.

Hakika fasahohin da kasar Sin ta samu ta hanyar raya kanta sun riga sun nuna cewa, samar da yanayi mai daidaito, da damar samun wadatar bai daya, tushe ne ga yunkurin samun ci gaban zaman al’umma mai inganci da dorewa.

Wannan shi ne dalilin da ya sa kasar Sin jaddada muhimmancin raya huldar abota dake iya samar da wani yanayi na daidaito tare da sauran kasashe, da kokarin kawar da gibin da ake samu tsakanin mabambantan kasashe ta fuskar ci gaban tattalin arizki, a cikin shawarar da kasar ta gabatar ta “kokarin tabbatar da ci gaban duniya”.

Abun da kasar Sin ke nema shi ma buri na bai daya na daukacin kasashe masu tasowa. Za mu iya tabbatar da cewa, za a yi kokarin kula da wannan buri, da neman cika shi, a taron kolin tsarin BRICS na wannan karo. (Bello Wang)

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Na Shirin Sake Kai Wa Jirgin Abuja Zuwa Kaduna Hari – DSS Ta Yi Gargadi

'Yan Bindiga Na Shirin Sake Kai Wa Jirgin Abuja Zuwa Kaduna Hari - DSS Ta Yi Gargadi

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.