• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Jigawa State,Mallam Umar Namadi, ya yi watsi da maganar gamyyar jam’iyyun adawa,inda yake cewa babu wani abin damuwa kan lamarin kafa ita gamayyar jam’iyyar adawar kafin babban zaben shekarar 2027.A wata hirar da ya Jaridar LEADERSHIP ta ranar Lahadi,yayi karin bayanin cewar maganar da ake cewa farinjinin na ja baya a Arewa ba maganar da za a saurara bace.

 

Amsa kan muradai sha biyu da ya bayyana lokacin da ya fara aiki a matsayin gwamnan Jigawa, ya bada amsar cewa ‘’Mun fara aiki a matsayinmu na gwamnati da burin da muke son cimmawa da kuma manufarmu domin bunkasa Jihar Jigawa ta samu babban ci gaba. Don haka ne muka bullo da muradai goma sha biyu wadanda suka kunshi dukkan bangarori,da suka hada da ilimi,harkar lafiya,tallafawa matasa su dogara da kansu, aikin gona,bangaren tsaro kudaden shiga, bunkasa kauyuka da kuma abubuwan more rayuwa. Bani ne ya dace na ce na yi wa kaina Alkalanci ba,wato ko mun yi abinda za a yabe mu ko akasin haka.Al’ummar Jigawa ne ya dace su yi Alkalanci kanmu.Amma kuma a namu auna ayyukanmu a matsayinmu na gwamnati,ina ganin mun samu ci gaba muna kuma alfahari da irin ci gaban da muka samu.Mun godewa Allah akan damar da ya bamu muka yi abinda ya bamu ikon yi.

  • Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
  • Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Muna tafiya da al’ummarmu a duk tsare-tsaren da muke yi.Ina da tabbacin cewar Jigawa ita kadai ce Jiha daya wadda take tafiya da al’ummarta a cikin ayyukan da take yi.Yadda muke shirya abin shi ne muna zuwa kowace karamar Hukuma inda muke taro da masu ruwa da tsaki, da dukkan wakilai kowace mazabar Kansilolin kowace Lahadi muna fada masu a matsayinmu na gwamnati, ayyukan da muka yi a shekaru biyun da suka gabata. Suna iya amincewa ko kuma su yi watsi da lamarin. A kowane bangare Kwamishina ne yake yin magana da mutanen kan ayyukan da muka yi. Tun da muna amfani ne da tsarin gwamnatin tarayya,muna cewa kowane Sanata da kuma dan majalisar Wakilai ya fadawa abubuwan da gwamnatin tarayya tayi masu ta hannunsu ‘yan majalisar.

 

Labarai Masu Nasaba

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Yanzu mun yi hakan a kananan Hukumomi takwas,zuwa Lahadi mai zuwa,zamu je ta tare. Zamu ci gaba da yin hakan har zuwa watan Nuwamba wanda hakan zai sa mu kammala da kananan Hukumomi 27. Zuwa yanzu ana ganin amfanin abinda aka yi,a duk kananan Hukumomi da muka ziyarta. Ina ganin mun yi rawar gani kan muradai 12,amma kamar yadda na ce al’ummar Jigawa sune wadanda ya dace su yi bayani kan irin ayyukan alkhairi da ci gaban da muka yi a matsayinmu na gwamnati.

 

Da aka yi ma shi maganar ya ware kashi 30 cikin 100 saboda bangaren ilimi,cewa ya yi ai Jigawa Jiha ce da take da manoma. Domin kuwa kusan kashi 85 zuwa 90 na yawan al’ummar manoma ne. Duk wata gwamnatin da take bukatar bunkasa tattali arzikin Jigawa da kuma jin dadin zamantakewar al’ummarta dole ne ta maida hankali kan aikin noma. Fannin akin noma shi yake samar da kashi 46 cikin 100 kudaden shiga na gwamnati a shekara.Ina farin ciki na fadi hakan cewar abinda muke yi yayi matukar bunkasa tattalin arzikin Jihar Jigawa, Gaskiya daukar matakin yin hakan ko shakka babu ya bunkasa jin dadin rayuwra al’ummarmu. Maganar gaskiya tsarin ya rage yawan wadanda suke zuwa Birane daga Kauyuka a cikin Jihar. Matasa yanzu sun amince da harkar noma ita ce babbar lamarin kasuwanci amma ba irin noman da mutum zai noma saboda shi kadai ba.Shi yasa muka bada muhimmanci da maida hankali kan noma da komawa gona.

Shi kuma ilimi wani babban ginshikin ci gaban rayuwa ne, ta kowane al’umma na duniya,amma ba sai Jihar Jigawa kawai ba.Shi,yasa muke ganin da akwai muhimmanci da kuma bukatar mu ilimantar da al’ummar mu, saboda kuwa mun san da zarar mun ilimantar da su, musamman ma matasa,wadanda sune za su kasance Shugabannin gobe. Shi yasa lamarin ilimi ma shi ma muka bashi muhimmanci. Domin ai muna da tsare tsaren na lamarin daya shafi ilimin. A babban bangaren ilimin, mun kaddamar da tsarin da ya shafi kafar sadarwa ta zamani a ilmance,ba,abin ya tsaya a samar da ilimi ga al’ummar ba,abin ma yana taimaka mana kan lamarin rashin zuwa aiki na Malaman makaranta.

Bugu da kari an amfana da shi wajen horon su Malaman.Zuwa yanzu,mun haorar da fiye da Malaman makaranta12,a karkashin shi tsarin.

Hakanan ma mun bullo da tsari na rage yawan yaran da basu zuwa makaranta, shi yasa ma muka bullo da tsarin Tsangaya, saboda kuwa Hukuma ce wadda ta fara aiki.Abinda muke yi shi ne mu tabbatar da duk yara a Jihar Jigawa,wadanda basu zuwa makaranta, an dawo da su makaranta.Mun samu nasrara yin hakan.Tsarin Tsangaya ya amince da masu ruwa da tsaki za a koyar da abubuwa uku:lamarin kirga da kuma yakar jahilci na kwana biyu,ilimin addii na kwana uku,sai kuma ilimin koyon sana’a na kwana daya.Tsarin makaranta na Tsangaya zai bada dukkannin abubuwan da suka zama dole wadanda kuma za su taimakawa masu karatu wajen samar da ilimin fasaha da kuma koyon sana’oi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Next Post

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Related

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato
Labarai

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

34 minutes ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

2 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

13 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

14 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

15 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

18 hours ago
Next Post
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.