• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Jere

Kwanturola-Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Isah Idris Jere, ya bayyana tsarin amfani da tantance bayanan shige da fice (MIDAS) a matsayin wani tsari da ya inganta iyakokin Nijeriya da sauya fasalin yadda ake ta’asa a iyakokin kasar nan. 

Jere, ga shaida haka ne wajen kaddamar da sabuwr cibiyar horaswa ta musamman ‘Training and Reference Centre’ a ranar Alhamis.

  • INEC Ta Fara Raba Kayan Aikin Zabe A Adamawa
  • Kungiyoyi Magoya Bayan Buhari-Osinbajo Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Zabi Atiku Na Jam’iyyar PDP

Ya kara da cewa, “Shirin MIDAS, ta hanyar amfani da shirin EABDS II tare da tallafin gwamnatin kasar Denmark ya kai ga asassa shirin a manyan wuraren sanya ido a filayen jirgin kasa da kasa guda biyar a Nijeriya ciki har da wannan cibiyar horon.”

Shugaban, ya ce duk da kalubalen da harkar shige da fice ke da fuskanta a a fadin duniya musamman a iyakoki, hukumarsa bisa goyon baya da taimakon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta samu nasarar fito da tsare-tsare da shirye-shiryen da suka taimaka sosai wajen dakile da shawo kan matsalolin da ake fama da su a kan iyakoki da harkar safara ba bisa ka’ida ba.

Shugaban na NIS, ya jinjina tare da yaba wa gwamnatin kasar Canada da Denmark kan tallafinsu wajen sabunta cibiyar horon inda ta ingata adadinta daga 15 zuwa 40 da suka kunshi cibiyar koyo ta Intanet, babban dakin horo, dakin adana bayanai, sashen kula da MIDAS da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

Ya ce, wannan taimakon tabbas zai taimaka wa hukumar wajen kara samun nasarori wajen kyautata tsaron iyakoki da shawo kan lamuran da suka shafi shige da fice.

Ya kuma kara da cewa an kuma sake samun wasu tallafin na’urorin sanya ido da suka hada da VSC da aka sanya a cibiyoyin aikin hukumar a filayen jirgi guda biyar wadanda suka taimaka sosai wajen saukin gane bayanan matafiya da taimaka wa wajen zurfafa bincike cikin sauki domin kyautata tsaron iyakokin kasar nan.

Kwanturolan ya kara da cewa, tabbas samar da cibiyar horaswar za ta taimaka musu wajen bai wa jami’ansu horon da ya dace da zai kara musu kwazo wajen gudanar da aikinsu.

Da yake jinjina kan tallafin da suka samu daga IOM da kasashen da suka taimaka, ya nanata aniyar Gwamnatin Tarayya a karkashin sanya idonsa wajen kara himma da kwazo wajen kyautata tsaron iyakokin Nijeriya zuwa ga aikin matakin aiki na kasa da kasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi

'Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.