ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin MIDAS Ya Kawo Sauyin Yadda Ake Kula Da Iyakoki —Jere

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Jere

Kwanturola-Janar na Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), Isah Idris Jere, ya bayyana tsarin amfani da tantance bayanan shige da fice (MIDAS) a matsayin wani tsari da ya inganta iyakokin Nijeriya da sauya fasalin yadda ake ta’asa a iyakokin kasar nan. 

Jere, ga shaida haka ne wajen kaddamar da sabuwr cibiyar horaswa ta musamman ‘Training and Reference Centre’ a ranar Alhamis.

  • INEC Ta Fara Raba Kayan Aikin Zabe A Adamawa
  • Kungiyoyi Magoya Bayan Buhari-Osinbajo Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Zabi Atiku Na Jam’iyyar PDP

Ya kara da cewa, “Shirin MIDAS, ta hanyar amfani da shirin EABDS II tare da tallafin gwamnatin kasar Denmark ya kai ga asassa shirin a manyan wuraren sanya ido a filayen jirgin kasa da kasa guda biyar a Nijeriya ciki har da wannan cibiyar horon.”

ADVERTISEMENT

Shugaban, ya ce duk da kalubalen da harkar shige da fice ke da fuskanta a a fadin duniya musamman a iyakoki, hukumarsa bisa goyon baya da taimakon shugaban kasa Muhammadu Buhari ta samu nasarar fito da tsare-tsare da shirye-shiryen da suka taimaka sosai wajen dakile da shawo kan matsalolin da ake fama da su a kan iyakoki da harkar safara ba bisa ka’ida ba.

Shugaban na NIS, ya jinjina tare da yaba wa gwamnatin kasar Canada da Denmark kan tallafinsu wajen sabunta cibiyar horon inda ta ingata adadinta daga 15 zuwa 40 da suka kunshi cibiyar koyo ta Intanet, babban dakin horo, dakin adana bayanai, sashen kula da MIDAS da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

Ya ce, wannan taimakon tabbas zai taimaka wa hukumar wajen kara samun nasarori wajen kyautata tsaron iyakoki da shawo kan lamuran da suka shafi shige da fice.

Ya kuma kara da cewa an kuma sake samun wasu tallafin na’urorin sanya ido da suka hada da VSC da aka sanya a cibiyoyin aikin hukumar a filayen jirgi guda biyar wadanda suka taimaka sosai wajen saukin gane bayanan matafiya da taimaka wa wajen zurfafa bincike cikin sauki domin kyautata tsaron iyakokin kasar nan.

Kwanturolan ya kara da cewa, tabbas samar da cibiyar horaswar za ta taimaka musu wajen bai wa jami’ansu horon da ya dace da zai kara musu kwazo wajen gudanar da aikinsu.

Da yake jinjina kan tallafin da suka samu daga IOM da kasashen da suka taimaka, ya nanata aniyar Gwamnatin Tarayya a karkashin sanya idonsa wajen kara himma da kwazo wajen kyautata tsaron iyakokin Nijeriya zuwa ga aikin matakin aiki na kasa da kasa.

Jere
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro
Manyan Labarai

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari
Labarai

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Jere
Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi

'Yan Bindiga Sun Harbe Shugaban APGA Har Lahira A Ebonyi

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

Sin Ta Kafa Manufar Shiga Sahun Manyan Kasashen Dake Da Karfi A Harkar Kera Motoci A Duniya Nan Da Shekarar 2030

September 11, 2026
Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

Sakkwato: Al’ummar Tambuwal Sun Yi Zanga-Zanga Kan Taɓarɓarewar Tsaro

September 11, 2026
Sanata yari

Gwarzon Ɗan Siyasa Na Shekarar 2026 Sanata Abdul’Aziz Abubakar Yari

September 11, 2026
Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

Kasar Sin Za Ta Taimaka Wajen Bunkasa Wadatar Makamashi Da Ci Gaba Mai Dorewa A Duniya

September 11, 2026
SAW

Ɗabi’un Annabi (SAW) Kan Abubuwa Na Al’adar Rayuwa

September 11, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Horar Da Malamai 250,000

September 11, 2026
Jere

Sojoji Sun Ceto Mutane 13 Da ’Yan Bindiga Suka Yi Garkuwa Da Su

September 11, 2026
Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

Taron BRICS: Shettima Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya Zuwa Indiya

September 11, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Gwamnan Shekara na 2026 Gwamna Caleb Manasseh Mutfwang

September 11, 2026
Jere

Idan Atiku Ya Janye, Za Mu Kula Da Shi Bayan Mun Yi Nasara – Kwankwaso

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.