• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Babban Sufeton ‘yan-sandan Nijeriya Tafa Balogun Ya Rasu

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Tsohon Babban Sufeton ‘yan-sandan Nijeriya Tafa Balogun Ya Rasu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Babban Sufeton ‘Yan-sandan Nijeriya, Mustapha Balogun, wanda aka fi sani da Tafa Balogun ya rasu bayan wata gajeruwar jinya a Lagos, yana da shekara 74.

BBC ta rawaito, Jaridar Punch ta ruwaito cewa wata kafa daga iyalansa ta tabbatar mata cewa ya rasu ne a yau Alhamis da misalin karfe 8:30 na daren nan a wani asibiti da ke Lekki a Jihar Lagos bayan wata gajeruwar jinya.

  • Gwamnatin Benuwai Ta Kafa Rundunar Tsaro Don Fatattakar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • 2023: APC Ta Ayyana Gwamna Lalong A Matsayin Daraktan Yakin Kamfen Din Tinubu

Balogun wanda aka haifa a ranar 8 ga watan Agusta na 1947 a garin Ila-Orangun da ke jihar Osun, shi ne Shugaban Rundunar ‘Yan-sandan Nijeriya na 21 a tarihi, bayan da aka nada shi a makumin a watan Maris na 2002.

Kafin ya kai wannan matsayi ya rike mukamai da dama da suka hada da mukaddashin kwamishinan ‘yan-sanda a JIhar Edo.

Ya kasance da Kwamishinan ‘yan-sanda na farko na Jihar Delta. Ya kasance Kwamishinan ‘yan-sanda na jihar Ribas da kuma Jihar Abia.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

Bayan da ya samu karamin mukami zuwa mataimakin babban sufeton ‘yan-sanda mai kula da shiyya ta daya aSure to Kano, daga nan ne likkafarsa ta yi gaba inda aka nada shi Sufeto Janar din a ranar 6 ga watan Maris na 2002.

A ranar 4 ga watan Afrilu na 2005 hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati EFCC ta gurfanar da shi a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja a kan zargin sata da halatta kudaden haram sama da dala miliyan 100 a tsawon shekara uku da ya yi a mukamin Sufeto-Janar.

Hukumar ta EFCC karkashin jagorancin Nuhu Ribadu ta tuhume shi da laifuka 70, inda daga bisani ya yi yarjejeniya ta bayar da wasu daga cikin kudade da abuibuwan da ake zarginsa da sace wa domin a sassauta masa, inda aka yanke masa hukuncin wata shida a gidan yari.

Mai shari’a Binta Nyako ta zartar da cewa kasancewar ya nuna nadama kuma wannan shi ne lokaci na farko da ya aikata laifi ta sassauta masa hukunci.

Ta umarci da ya biya Naira dubu 500 a kan kowanne daga cikin laifuka takwas da ya amince ya aikata daga cikin 56 da suka shafe shi kai tsaye, tarar da ta kama jumulla Naira miliyan 4.

Mai shariar ta kuma yanke masa hukuncin zaman gidan yari na wata shida a kan kowanne daga cikin laifukan 8, wadanda zai yi su tare.

Shariar tasa ta dauki hankali inda a wani lokaci ya fadi a kujerar da ya ke a ranar 29 ga watan Yuni na 2005 a kotun.

An sake shi a ranar 9 ga watan fabrairu na 2006 bayan da ya kammala wa’adin, wani daga ciki a babban asibitin kasa na Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Benuwai Ta Kafa Rundunar Tsaro Don Fatattakar ‘Yan Bindiga A Jihar

Next Post

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Related

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

31 minutes ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

3 hours ago
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
Labarai

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

3 hours ago
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

7 hours ago
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

8 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.