• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Babban Sufeton ‘yan-sandan Nijeriya Tafa Balogun Ya Rasu

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Tsohon Babban Sufeton ‘yan-sandan Nijeriya Tafa Balogun Ya Rasu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Babban Sufeton ‘Yan-sandan Nijeriya, Mustapha Balogun, wanda aka fi sani da Tafa Balogun ya rasu bayan wata gajeruwar jinya a Lagos, yana da shekara 74.

BBC ta rawaito, Jaridar Punch ta ruwaito cewa wata kafa daga iyalansa ta tabbatar mata cewa ya rasu ne a yau Alhamis da misalin karfe 8:30 na daren nan a wani asibiti da ke Lekki a Jihar Lagos bayan wata gajeruwar jinya.

  • Gwamnatin Benuwai Ta Kafa Rundunar Tsaro Don Fatattakar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • 2023: APC Ta Ayyana Gwamna Lalong A Matsayin Daraktan Yakin Kamfen Din Tinubu

Balogun wanda aka haifa a ranar 8 ga watan Agusta na 1947 a garin Ila-Orangun da ke jihar Osun, shi ne Shugaban Rundunar ‘Yan-sandan Nijeriya na 21 a tarihi, bayan da aka nada shi a makumin a watan Maris na 2002.

Kafin ya kai wannan matsayi ya rike mukamai da dama da suka hada da mukaddashin kwamishinan ‘yan-sanda a JIhar Edo.

Ya kasance da Kwamishinan ‘yan-sanda na farko na Jihar Delta. Ya kasance Kwamishinan ‘yan-sanda na jihar Ribas da kuma Jihar Abia.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Bayan da ya samu karamin mukami zuwa mataimakin babban sufeton ‘yan-sanda mai kula da shiyya ta daya aSure to Kano, daga nan ne likkafarsa ta yi gaba inda aka nada shi Sufeto Janar din a ranar 6 ga watan Maris na 2002.

A ranar 4 ga watan Afrilu na 2005 hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati EFCC ta gurfanar da shi a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja a kan zargin sata da halatta kudaden haram sama da dala miliyan 100 a tsawon shekara uku da ya yi a mukamin Sufeto-Janar.

Hukumar ta EFCC karkashin jagorancin Nuhu Ribadu ta tuhume shi da laifuka 70, inda daga bisani ya yi yarjejeniya ta bayar da wasu daga cikin kudade da abuibuwan da ake zarginsa da sace wa domin a sassauta masa, inda aka yanke masa hukuncin wata shida a gidan yari.

Mai shari’a Binta Nyako ta zartar da cewa kasancewar ya nuna nadama kuma wannan shi ne lokaci na farko da ya aikata laifi ta sassauta masa hukunci.

Ta umarci da ya biya Naira dubu 500 a kan kowanne daga cikin laifuka takwas da ya amince ya aikata daga cikin 56 da suka shafe shi kai tsaye, tarar da ta kama jumulla Naira miliyan 4.

Mai shariar ta kuma yanke masa hukuncin zaman gidan yari na wata shida a kan kowanne daga cikin laifukan 8, wadanda zai yi su tare.

Shariar tasa ta dauki hankali inda a wani lokaci ya fadi a kujerar da ya ke a ranar 29 ga watan Yuni na 2005 a kotun.

An sake shi a ranar 9 ga watan fabrairu na 2006 bayan da ya kammala wa’adin, wani daga ciki a babban asibitin kasa na Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Benuwai Ta Kafa Rundunar Tsaro Don Fatattakar ‘Yan Bindiga A Jihar

Next Post

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

7 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

8 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

9 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

14 hours ago
Tsohon
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

14 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

15 hours ago
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.