ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Babban Sufeton ‘yan-sandan Nijeriya Tafa Balogun Ya Rasu

by Muhammad
4 years ago
Tsohon

Tsohon Babban Sufeton ‘Yan-sandan Nijeriya, Mustapha Balogun, wanda aka fi sani da Tafa Balogun ya rasu bayan wata gajeruwar jinya a Lagos, yana da shekara 74.

BBC ta rawaito, Jaridar Punch ta ruwaito cewa wata kafa daga iyalansa ta tabbatar mata cewa ya rasu ne a yau Alhamis da misalin karfe 8:30 na daren nan a wani asibiti da ke Lekki a Jihar Lagos bayan wata gajeruwar jinya.

  • Gwamnatin Benuwai Ta Kafa Rundunar Tsaro Don Fatattakar ‘Yan Bindiga A Jihar
  • 2023: APC Ta Ayyana Gwamna Lalong A Matsayin Daraktan Yakin Kamfen Din Tinubu

Balogun wanda aka haifa a ranar 8 ga watan Agusta na 1947 a garin Ila-Orangun da ke jihar Osun, shi ne Shugaban Rundunar ‘Yan-sandan Nijeriya na 21 a tarihi, bayan da aka nada shi a makumin a watan Maris na 2002.

ADVERTISEMENT

Kafin ya kai wannan matsayi ya rike mukamai da dama da suka hada da mukaddashin kwamishinan ‘yan-sanda a JIhar Edo.

Ya kasance da Kwamishinan ‘yan-sanda na farko na Jihar Delta. Ya kasance Kwamishinan ‘yan-sanda na jihar Ribas da kuma Jihar Abia.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Bayan da ya samu karamin mukami zuwa mataimakin babban sufeton ‘yan-sanda mai kula da shiyya ta daya aSure to Kano, daga nan ne likkafarsa ta yi gaba inda aka nada shi Sufeto Janar din a ranar 6 ga watan Maris na 2002.

A ranar 4 ga watan Afrilu na 2005 hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati EFCC ta gurfanar da shi a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja a kan zargin sata da halatta kudaden haram sama da dala miliyan 100 a tsawon shekara uku da ya yi a mukamin Sufeto-Janar.

Hukumar ta EFCC karkashin jagorancin Nuhu Ribadu ta tuhume shi da laifuka 70, inda daga bisani ya yi yarjejeniya ta bayar da wasu daga cikin kudade da abuibuwan da ake zarginsa da sace wa domin a sassauta masa, inda aka yanke masa hukuncin wata shida a gidan yari.

Mai shari’a Binta Nyako ta zartar da cewa kasancewar ya nuna nadama kuma wannan shi ne lokaci na farko da ya aikata laifi ta sassauta masa hukunci.

Ta umarci da ya biya Naira dubu 500 a kan kowanne daga cikin laifuka takwas da ya amince ya aikata daga cikin 56 da suka shafe shi kai tsaye, tarar da ta kama jumulla Naira miliyan 4.

Mai shariar ta kuma yanke masa hukuncin zaman gidan yari na wata shida a kan kowanne daga cikin laifukan 8, wadanda zai yi su tare.

Shariar tasa ta dauki hankali inda a wani lokaci ya fadi a kujerar da ya ke a ranar 29 ga watan Yuni na 2005 a kotun.

An sake shi a ranar 9 ga watan fabrairu na 2006 bayan da ya kammala wa’adin, wani daga ciki a babban asibitin kasa na Abuja.

Tsohon
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

Ma’aikatar Tsaron Sin Ta Yi Bayani Game Da Matakan Soji Da Kasar Ta Dauka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.