• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tun Ina Yaro Harkar Fim Ke Birge Ni —Abba Harara

by Sulaiman
3 years ago
in Nishadi
0
Abba Harara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin Shahararrun Marubutan fina-finan Hausa, kana matashi mai shiryawa wanda ya shafe shekaru goma cikin masana’antar Kannywood wato ABBA ABUBAKAR MUHAMMAD Wanda aka fi sani da ABBA HARARA ya bayyana dalilinsa na maida hankali ga shirya fin nasa na kansa, har ma da wasu batutuwan da suka shafi sana’arsa ta fim. Ga dai tattaunawar tare da Wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Ya sunan Malamin?
Sunana Abba Abubakar Muhammad amma an fi sanina da Abba Harara.

Ko za ka fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?
Toh an haifeni A Garin Kano Unguwar Gama ‘Brigade’ nayi ‘Primary’ da ‘Secondry’ A Suntulma Dake Unguwar Gama, na tsaya iya ‘Secondry’ ban ci gaba ba sai kuma Allah ya kawo ni masana’antar Kannywood.

Cikin sunanka na ji an hada da Harara, A ina ka samo sunan Abbah Harara?
Na samu sunan a wajen Aisha Aliyu Tsamiya, ba na mantawa ita ce ta saka min kuma cikin ikon Allah ya bini.

Wanne rawa kake takawa a cikin masana’antar Kannywood?
Ina taka rawa guda 2 a cikin masana’antar Kannywood. Na 1 ni Marubuci ne, na 2 kuma ni mai shiryawa ne wato ‘Producer’.

Labarai Masu Nasaba

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood?
Tun ina yaro harkar fim take birge ni kwarai da gaske.

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?
Abin dai kam sai godiya duk da gaskiya ni ban sha wuya wajen shiga ba.

Za ka yi kamar shekara nawa cikin masana’antar?
Zan yi kamar shekara 10.

Ga ka marubuci kuma mai shiryawa, toh tun a farkon da ka fara rubutun kana shirya fim ne ko kuwa iya rubutun kake daga baya kuma ka dora da shiryawa?
Tun farko ni marubuci ne ban taba tunanin ma zan kasance daga cikin masu shirya fina-finai ba, Amma cikin ikon Allah sai na samu kaina a wannan bangaren.

Taya za ka yi wa masu karatu bayanin yadda aka yi har ka fara shirya fim?
Akwai lokacin da za ki ga wasu daga cikin mutanenmu basa daukar labarinka yadda ka tsara shi to wannan yana kashe martabar labari shi ne kawai abin da ya bani kwarin gwiwar nima na soma shirya nawa da kaina.

Farkon da za ka fara shirya fim naka na kanka shin ka nemi taimakon wani ko kuwa kai tsaye ka fara?
A’a! Ban nemi taimakon kowa ba.

Ko akwai wani dan kalubale da ka fuskanta a lokacin, ganin cewar shi ne farkon farawar ka, musamman yadda za ka harhado kan su Jaruman da kake son su taka rawa cikin fim din?
Toh! kin san ba a rasa matsala a yayin farkon somawa amma Alhamdulillah gaskiya sai godiya kawai.

Mu koma batun rubutu, lokacin da za ka fara ka nemi taimakon wani ne ko kuwa da kanka ka zauna ka fara rubutawa?
Gaskiya akwai wanda ya shige min gaba a harkar rubutu shi ne ma ya koya min yadda ake rubutun labarin fim ba na taba mantawa, Sunanshi Sani Ata.

Wanne fim ka fara rubutawa kuma wanne ka fara shiryawa ?
Fim din da na soma rubutawa shi ne Ranar Suna, wanda na soma shiryawa kuma shi ne Malamin Kauna.

Kamar wadanne Jarumai ne suka fito cikin fim din?
Ali Rabi u Ali Daddy da Aisha Aliyu Tsamiya da Tanimu Akawu da Isyaku Jalingo.

Nawa ne adadin fina-finan da ka rubuta da kuma wanda ka shirya?
Wanda na rubuta ba za su wuce 50 ba wanda kuma na shirya ba za su wuce 5 ba.

Wanne abu ne ya fara baka wahala lokacin da za ka fara rubutu da kuma lokacin da ka fara kokarin shirya fim da kanka?
Toh gaskiya lokacin da zan rubutu na kan kwana na wuni ban iya rubuta komai ba saboda duk abin da ya kasance nazari ne to yana bukatar dogon tunani. Haka da na soma kokarin shirya fim na kaina na sha wahala saboda abu ne wanda ba ka taba yi ba sai kuma ka zo za ka yi to za ka fuskanci abubuwa da dama.

Toh ya batun dawowar kudaden da aka kashe, musamman bangaren shirya fim din?
A gaskiya kudi basa dawo wa a harkar fim kawai muna yi ne saboda sabo kuma kawa zuci saboda harkar fim tana da shiga rai.

Kamar yanzu da fim ya koma kan ‘You tube’ ake Siris fim ya kuke iya fidda kudadenku har kuke biyan sauran Jaruman da za su fito cikin fim din, ko kuwa yanzu ba biya ake yi ba kawai ana yi ne ya fi ba a yi ko kuwa?
Dole za ka biya Jarumi sannan idan ‘YouTube’ din ka ya kai wani mataki za a soma biyanka duk da hakan baya dawo da kudin da ka kashe sai dai ka dan samu abin da ka samu kawai.

Kamar shi rubutun fim din, idan kuka rubuta siyar wa kuke yi ga masu shiryawa, ko kuwa kyauta kuke bayar wa ganin ku ne marubutan duk kuna tare?
Siyar wa muke yi ko kuma furodusa ya ce ka yi masa rubutu ya biya ka ba kyauta bane.

A cikin naka rubutun fim din wanne ne ka siyar da shi da tsoka wanda ba za ka taba mantawa ba
Akwai wani sunansa ATM.

Ko za ka iya fado wa masu karatu sunayen fina-finan da ka rubuta ko da kadan ne?
Akwai Fauwaz, Farida Nabil, Sirrin Zuciya, Bani da laifi, Makullin Zuciya, Maraicin ‘Ya Mace, Ruhin Mijina, Sadeek Sanam, da dai sauransu.

Za mu ci gaba mako me zuwa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ranar Dimokuradiyya: Nasarar Bola Tinubu Alama Ce Ta Hadin Kan Nijeriya —Bagudu

Next Post

Zargin Tayar Da Tarzoma: An Damke Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Kogi

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

3 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

1 week ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

2 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

3 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

1 month ago
Next Post
Zargin Tayar Da Tarzoma: An Damke Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Kogi

Zargin Tayar Da Tarzoma: An Damke Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Kogi

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.