• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tun Kafin A Samu Masana’antar Kannywood Nake Harkar Fim – Lilisco

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Nishadi
0
Tun Kafin A Samu Masana’antar Kannywood Nake Harkar Fim – Lilisco
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daya daga cikin manyan jarumai da aka dade ana damawa dasu a masana’antar Kannywood Shuaibu Idris wanda akafi sani da Lilisco ya bayyana abubuwa da dama da suka danganci rayuwarshi ta masana’antar Kannywood wadda ya shafe fiye da shekara 30 a cikinta.

 

Lilisco wanda ya yi shura a masana’antar Kannywood daga jarumi mai rawa da soyayya kafin ya rikide zuwa jarumi mai fitowa matsayin Dan Sandan hukumar yan sanda ta Nijeriya inda kuma yakan taka muhimmiyar rawa a duk lokacin da ya fito a irin wannnan aiki na jami’in tsaro, Lilisco ya ce ba shi ne ya zabi wannan role din ba amma tunda masu shirya fina-finai sun ga ya dace da wannan matsayi babu abinda ya dace ya yi illa ya yi iya kokarin shi wajen burge masu kallo a duk lokacin da ya fito a cikin fim.

  • Na Fi Jin Dadin Rubutu In Na Gaji Tibis – Maryam Faruk
  • Neymar Zai Yi Jinyar Mako Biyu Bayan Ya Sake Samun Rauni

Lilisco a wata hira da ya yi da jaruma Hadiza Gabon a cikin shirinta mai suna Gabon’s Room Talk Show ya ce asalinsa ma’aikaci ne a hukumar tarihi da raya al’adun gargajiya ta jahar Kano (Kano State History And Cultural Bureau) wanda hakan ne ya bashi kwarin gwiwar cewa zai iya wannan sana’a ta fim domin kuwa babban abinda ya iya a wancan lokacin shi ne rawa, wadda akan yi kala kala kama daga da gargajiya da kuma ta zamani.

 

Labarai Masu Nasaba

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

Ya ci gaba da cewar tun kafin a samu wannan masana’antar ta Kannywood da nike alfahari da ita a yanzu na fara wannan harka ta Fim domin kuwa an taba daukata domin yin aikin wani fim a garuruwan Bauchi da Jos a shekarar 1991 shekaru 3 kafin samun wata masana’antar harkar fim a nan Jihar Kano.

 

Bayan an fara anan gida Kano sai na nuna sha’awar nima ina son in shiga harkar kuma cikin iyawar Allah na shiga da kafar dama, domin kuwa a wancan lokacin akwai wani fim da na yi a shekarar 1997 wanda ya samu daukaka sosai ya burge mutane har ya sa da dama daga cikin manyan masu shirya fim a wancan lokacin suka nuna sha’awar saka waka da rawa a fina finansu in ji shi.

 

Ana nan har furodusan shirin Sangaya ya bukaci in koya wa jaruman da zai saka a cikin shirin rawa, wadanda suka hada da Ali Nuhu, Fati Muhammad da kuma marigayiya Hauwa Ali Dodo, da haka ne ya zamana duk wani fim da za a yi sai an nemi in koyar da jaruman fim din rawar waka, wanda ni kuma a lokacin sai naga cewar da in ci gaba da yin fina-finai nawa na kaina ai kara in tsaya a wannan sabon aiki da nasamu tunda dama dai ni mai koyar da rawa ne inji Lilisco.

 

Da yake amsa tambaya a kan dalilin da yasa yanzu harkar gidajen sinima suka daina yin tasiri, Lilisco ya ce daga cikin abinda ya tauye harkar sinima a yanzu akwai shigowar media da kuma wayoyin hannu da suka yawaita a hannun mutane inda ya ce a lokacin baya idan sabon fim ya fito zakaga mutane suna tururuwar shiga gidajen sinima domin kallon sabbin fina-finai amma yanzu mutum na gidansa zaune zai saka data kawai ya kalla a YouTube ko wata manhajar yanar gizo ba tare da ya tafi sinima ba.

 

Hakan yasa yanzu mutane suka daina zuba kudadensu a harkar gidajen sinima domin kuwa koda ka saka kudi ka bude gidan sinima ba lallai bane ka iya mayar da kudaden da ka kashe ba kamar a lokacin baya da babu wata hanyar samun kudi a masana’antar Kannywood kamar sinima ba.

 

Daga karshe Shuaibu Idris ya karyata wadanda ke cewa jarumai mata a masana’antar Kannywood basu son zaman aure, inda ya ce ko kusa wannan magana babu kamshin gaskiya a cikinta domin kuwa yanzu haka matarsa ‘yar masana’antar Kannywood ce gaba da baya amma kuma sun shafe shekaru fiye da 20 a tare ba tare da wata matsala ba.

 

Maganar da ake yi na cewa jarumai mata a masana’antar Kannywood basu son zaman aure ba gaskiya ba ne don yanzu haka ina zaune da matata wadda take yar masana’antar Kannywood gaba da baya lami lafiya tsawon shekaru fiye da 20 ba tare da wata matsala ba,mun haifi ‘ya’ya biyar tare da ita sannan kuma tana kyautata mani bakin gwargwado nima ina kyautata mata iya zarafi na saboda haka idan naji wasu na irin wadannan maganganu sai dai inyi kurum saboda a ganina sai aure 1000 na wadanda ba yan Kannywood ba ya mutu kafin auren jarumar Kannywood daya ya mutu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jarin Da Ake Zubawa A Fannin Bincike Da Samar Da Ci Gaban Manyan Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Haura Yuan Tiriliyan 1

Next Post

Sin Ta Sanar Da Shata Iyakar Yankinta Na Teku Daura Da Tsibirin Huangyan

Related

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe
Nishadi

Ya Kamata Mata ‘Yan Fim Su Rike Mutuncin Kansu – Aisha Tafida Gombe

5 days ago
Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje
Nishadi

Saboda In Nuna Wa Duniya Asalin Al’adar Bahaushe Ya Sa Na Fara Fina-finan Turanci A Arewacin Nijeriya – Jammaje

2 weeks ago
Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda
Nishadi

Daga Kaina An Gama Harkar Fim A Zuri’ata – Moda

2 weeks ago
Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri
Manyan Labarai

Rarara Zai Angwance Da Aisha Humaira Yau A Maiduguri

2 weeks ago
Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan
Nishadi

Jerin Manyan Jaruman Fim Da Nijeriya Ta Rasa A Yan Shekarun Nan

3 weeks ago
Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?
Nishadi

Me Ya Janyo Jifan Mawaka A Arewacin Nijeriya?

4 weeks ago
Next Post
Sin Ta Sanar Da Shata Iyakar Yankinta Na Teku Daura Da Tsibirin Huangyan

Sin Ta Sanar Da Shata Iyakar Yankinta Na Teku Daura Da Tsibirin Huangyan

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.